بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
Hausa

Mutuwa da Alamomin Tashin Duniya

Engr. Baba Magaji

Mutuwa da Alamomin Tashin Duniya

الموت وعلامات الساعة

Engr. Baba Magaji

1

  

2

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page i BISMILL ÃHI RAHM ÃNIR RAHĨM.

Dukkan g õdiya ta tabbata ga Allah (S.W.A) Ubangijin d a Ya halicci halittu Ya hali cci rãyuwa Ya halicci

mutuwa. Tsira da aminci su tabbata ga s hugaba, masoyi, mafi ky ãwon halitta da ɗabi’a wanda

sanadin zuwansa ne mutane su ka fita daga cikin duf fan jahilci , (Sallal lãhu alaihi wa sa llam) da

iyãlensa da sahabbansa (R.A) .

Bayan haka, wannan littafi ne wan da marub ũcinsa ya samu ilmin rub ũta shi (kuma ya rub ũta shi) ,

watanni ka ɗan baya n yayi wani mafarki a ranar 13/Rama dan/1420 Hijra , (20/12/1999).

Na kwafa daga memo na marub ũcin “ Yau 20/12/99 – 13 Ramadan 1420, nayi mafarki ana karanta

mini wani littafi da Annabi (S.A.W) ya wallafa. Naga littafi n, sunansa ALKIYAMA, sannan a gefe n

sunan Alkiyamar an rubuta : “ka anna masjidan ”.

A lõkacin shekar ũna basu wuce 2 1 ba, nã rubũce lãbarin Alkiy ãma kaf (illa mash ã Allahu) . Tun a

lõkacin, Dauda Madaki Waziri yã yi mini bĩtar rubũtun harshen hausa , Sheik Faruq Che ɗi (sãhibin

Sheik Umar Sani Fa ge) ya duba littafin , amma ban samu tallafin baza litt ãfin ta hanyar launching ba.

Na raba litt ãfin kashi biyu, na farko n ã bãshi suna “Al-mautu wa al ãmãtis S ã’a” na biyu n ã bãshi

sũna Yaumul Ƙiyãma. Na daɗe da shigar da Yaum ul Ƙiyama cikin computer amma wannan na farkon

nã shigar dashi computer, kuma n ã gyara (editing) a cikin watan shawwal 1438 A.H (2017) .

Idan Allah (S .W.A) Yã bãni ikon maida wannan litt ãfi da harshen t ũranci, sannan l ãrabci, sai kuma

batun gy ãran (editing) Yaumul Ƙiyãma.

Daga ƙarshe (in Allah (SWA) Yã yarda, cikin ikonsa) zan rubũta film script a shirya FILM

(documentry ) na rãnar T ãshin Ƙiyama (wanda bai sa ɓawa sunna h ba) k õwa yaga yadda al ’amarin zai

kasance.

اق ْرَأْكِتَابِ ى كَفَى بِن َفْسِكَ الْي َوْمَ عَلَيْكَ حَسِيبًا

"Karanta Litt ãfi na. Ranka y ã isa ya zama mai hisãbi a kanka a yau."

(Iqtibas)

Nã dũba littafai marasa yawa l õkacin rub ũtu da gy ãra (editing) na wannan littafi, banyi amf ãni da

bayãnin wani shehi da bai dangant a bay ãninsa da Manzon Allah (SAW) k õ Salafus S ãlihĩna ba! ‘Yan

misãlai kaɗan d a na shigar dasu, fahimta ta ce ! Idan sun d ãce da wur ãren sai a riƙa da alheri. Idan

nã kuskure, sai ku d ãwo dani hanya. Allah dai Shi ne Mafi sani ,(SWA) , kuma Sh ĩ muke r õƙo Ya yãfe

mana kur ãkurenmu, Ya sa mu cika da ĩmãni akan sunnar manzonSa (SAW).

Jũmu’a: 5 Zul-Qada 1348

(28/7/2017)

Engr. Baba Magaji .

3

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 1

Da sunan Allah Mai Rahama mai Jin ƙai, Tsira da aminci su tabbata ga shugabanmu

Annabi Muhammadu

Mutuwa suna ne da ake amfani dashi wajen nuna fitar r ãyi (ko rũhi) daga gangar jiki.

Idan aka ce: Zaidu y ã mutu, ana nufin Zaidu y ã rasa rãyinsa.

Rãyi (ko rũhi) halitta ne da Allah (SWA) Ya barwa kanSa sanin b ãyanin sifarsa. Babu

mai iya b ãyanin banbancin sifar rũhin namiji da sifar rũhin mace. Abin sani kawai,

rũhi yana cikin gangar jikin halittar da take rãyuwa . "…Rũhi daga al´amarin

Ubangijina ne, kuma ba a bã ku (kõme) ba daga ilmi fãce ka ɗan." (17:85)

Haka kuma, Mutuwa sũna ne na halittar da take cire r ãyi (ko rũhi) na mutum ko aljani

ko waninsu, a lõkacin da kwanan da aka ɗeba masa a d ũniya ya ƙãre.

Bãbu sãɓãni, ko marar addini (pagan ) ya yarda da cewar: “dukkan mai rãyi, wata

rãna zai kasance matacce .”

Sãɓãnin kawai, sã ɓãnin imãni da abubuwan da za su kasance b ãyan mai rãyi ya mutu

ne. “Kuma (mushirikai) suka ce: " Bãbu kõme fãce rãyuwarmu ta dũniya; munã

mutuwa kuma munã rãyuwa (da h aihuwa) kuma bãbu abin da yake halaka mu sai

zãmani." Alhãli kuwa (ko da suke fa ɗar maganar) bã su da wani il imi game da

wannan, bã su bin kõme face zato1.

Wassu daga cikin mushirikan z ãmani suka ce idan mutum ya mutu za‟a sake haifansa

a wani sãshe na dũniya, suka ce: " Rãyuwa ba ta zama ba fãce rãyuwarmu ta dũniya,

munã mutuwa kuma munã rãyuwa, kuma ba mu zama wa ɗanda ake tãyarwa ba."2

Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne. Kuma ana cika muku ijãrõrinku kawai ne a

Rãnar Ƙiyãma. To, wanda aka nĩsantar daga ba rin wuta, kuma aka shigar da shi

Aljanna, to, lalle ne yã tsĩra. Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba fãce jin dã ɗin

rũɗi. (3:185)

(Allah) Shi ne Wanda Ya halitta mutuwa da rãyuwa domin Ya jarraba ku (mutane da

aljannu), Ya nũna wãye daga cikinku ya fi kyãwon aiki, (Allah) Shi ne Mabuwãyi,

Mai gafara. (67:2)

1 . Alkur‟ani 45:24

2 . Alkur‟ani 23:37

4

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 2 Manzon Allah (SAW) ya ce “Allah Mai girma Ya samar da ɗan-Adam tare da

mutuwa, kuma Ya sanya dũniya gidan rãyuwa sannan gidan mutuwa. Kuma Ya sanya

Lãhira gidan sakama ko sannan gidan wanzuwa (gidan rãyuwa har abada).3

An yo hik ãya daga ɗan-Abbas (R.A) , da Kalbiyyu da Muqatil: cewa ita mutuwa da

rãyuwa jinsin halitta ne guda biyu. Sai aka sanya mutuwa ta zama mai surar

(kamannin) r ãgo. B ã ta wucewa ta wuri, ko aji ƙamsh inta face sai an mutu. Kuma aka

halicci rãyuwa da surar g õɗiya. Ita ce Mal ã‟ika Jibirilu da Annabawa (A.S) suke hawa.

Gõɗiyar tã ɗara Jãki ba ta kai alfadari ba, jefa ƙafarta iya ganin idanu. B ã ta wucewa ta

gefen abu yaji ƙamshinta sai ya rayu. Ƙasar t ãkunta ne S ãmiri ya dam ƙa ya jefa a

gunkin ɗan-maraki sai ya rayu!4

Alal haƙiƙa, Allah (SWA) Shi Yake r ãyãwa, Yake kashewa. Ita dai mutuwa, za a

misalta ta ne da r ãgo a ran ar lãhira, kuma a yankata a kan sir ãɗi.

Allah ne ke kar ɓar rãyuka a lõkacin mutuwarsu, da wa ɗannan da ba su mutu ba, a

cikin barcinsu. Sa´an nan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki

gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga

mutãne wa ɗanda ke yin tunãni. (39:42)

Karɓan rãyuka a cikin bar ci shine mutuwa ƙarama, Amma mutuwa babba itace wacce

ake ganin abinda ake gani!

Allah (SWA) Shi Y ake cire rũhin duk wanda zai mutu, amma Yana wakilta Mal ã‟ika

Azrã‟ilu ne yaje ya ciro rãyin wanda kwanan nasa ya ƙare.

Ka ce: " Malã’ika n mutuwa ne wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke kar ɓar

rãyukanku. Sa´an nan zuwa ga Ubangijinku ake m ãyar da ku." (32:11)

A lõkacin da Malã‟ika Azrã‟ilu yazo ɗaukan rai, sai muce mutuwa t ã zo. Malã‟ika n

ɗaukan rai yakan zo ɗaukan rãyi ne da ɗãya daga cikin siffofin mutuwa guda biyu.

A lõkacin da mutuwa tazo ɗaukan rãyin mutumin kirki (m ũmini), z ã ka ganta da siffar

mutum, sau rayi kyakkyawa, ma‟ab õcin ƙamshi mai d ãɗi, sanye da far ãren tuf ãfi.

Amma idan mutuwa tazo ɗaukan rãyin kãfiri, da z ã ka ganta da siffar wani ba ƙin

mutum mai tsawon gaske. Kayinsa yana kusa da sama, b ãkinsa yana balbalar da wuta.

3. Duba tafsirin Qurdabi, tafsirin 67:2, domin ƙarin bayani.

4.Duba tafsir in Qurdabi , tafsirin 67:2.

5

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 3 Kõwane g ãshin da yake jikin wannan mutum za ka ga wani mutum yana balbalar da

wuta ta b ãkinsa. A ta ƙaice mutum ne mai tsananin duhu, d uk jikinsa mutane ne masu

siffarsa, harshen wuta yana fita ta b ãkinsu da kunnuwansu.

Dã balã‟i da baƙin ciki zai ta ƙaita (bã ƙãrãwa) ga kãfiri a lõkacin da mutuwa ta zo

masa, d ã wannan sũra ta mutuwa t ã isar masa.5 Allah (SWA) Ya kiy ãye mu.

Allah Ma ɗaukakin Sarki Y ã halicci Mutane, Kõwane mutum Allah (SWA) Yã fitar da

shi dũniya yana j ãriri, sannan Allah (SWA) Yã fitar da shi ne domin ya isa ga cikar

ƙarfin sa- shekara arba‟in, sannan ya zama tsoho (dattijo), sannan ya kai ga wani ajali

wanda zai mutu.

Kõwane mutum ba zai kauce ma ɗãyan jerin nan ba, sai dai k ãfin ya zo cikar ƙarfi ko

tsũfa, Allah (SWA) Yana iya gab ãtar masa da ajalinsa, sai mutum ya s ãmu kansa daga

cikin matattu.

Shĩ ne (Allah) Wanda Ya halitta ku daga tur ɓãya, sa´an nan d aga maniyyi, sa´an nan

daga sãren jini, sa´an nan Ya fitar da ku kunã jãrĩri, sa´an nan dõmin ku isa ga cikar

ƙarfinku sa´a n nan dõmin ku kasance tsõfaffi, kuma daga cikinku, akwai wanda ake

karɓar ransa a gabãnin haka, kuma dõmin ku isa ga ajali ambatacce , kuma

ɗammãninku ko zã ku hankalta. (40:67)

Garga ɗi:

Shĩ ne Wanda Ya sanya ku mãsu maye wa junã, a cikin ƙasã. To, wanda ya kãfirta, to,

kãfircinsa yanã a kansa. Kuma kãfircin kãfirai bã ya ƙãra musu kõme fãce baƙin jini,

kuma kãfircin kãfirai bã ya ƙãra musu kõme face hasãra. (35:39)

Wanda ya kasance yanã nufin mai gaggãwa, ( dũniya ) sai Mu gaggauta masa a cikinta,

abin da Muke so ga wanda Muke nufi, sa´an nan kuma Mu sanya masa Jahannama, ya

ƙõnu da ita, yanã abin zargi kuma abin tunku ɗewa.

Kuma wanda y a nufi Lãhira, kuma ya yi aiki sabõda ita ir in aikinta alhãli kuwa yanã

mũmi ni, to, waɗannan aikinsu ya kasance gõdadde. (17:18 -19)

Yã ku wa ɗanda suka yi ĩmãni! Ku lazimci rãyukanku, wanda ya ɓace bã zai cuce ku

ba idan kun shiryu, zuwa ga Allah makõmarku take gabã ɗãya. Sa´an nan Ya bã ku

lãbari ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa. (5:105)

a kowace al‟umma akwai ajalinta, sannan idan ajalinta ya zo ba z ã ta samu ƙãrin

lõkaci ba. Cikin kowace da ƙiƙa (ko awa) , ana iya samun dubban mutane suna

5. A duba tafsi rin ɗabari , tafsi rin 2:260. G

6

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 4 mutuwa dag a wurare daban -daban na dũniya . Kuma ba a musu jinkiri ko wani ya riga

abokinsa ga ajali!

وَلِكُلّْ أُمَّةٍ أَجَلٌ فَإِذَا جَاءَ أَجَلُهُمْ َلَ يَسْتَأْخِرُوفَ سَاعَةً وََلَ يَسْتػَقْدِمُوفَ

Kuma ga kõwace al´umma akwai ajali. Sa´an nan idan ajalinsu ya j e, bã zã a yi

musu jinkiri ba, sa´a guda, kuma bã zã su gabãce shi ba. (7:34)

Garga ɗi:

…Sai ku yi tsere zuwa ga ayyukan alheri, inda kuka kasance duka Allah zai zo da ku

gabã ɗãya. Lalle ne Allah, a kan kõme, Mai ĩkon yi ne. (2:148)

Kuma bã ya yiwuwa ga wa ni rai ya mutu fãce da iznin Allah, wa´adi ne mai

ƙayyadadden ajali. Kuma wanda yake nufin sakamakon dũniya Muna bã shi daga gare

ta. Kuma wanda ke nufin samakon Lãhira Muna bã shi daga gare ta. Kuma zã Mu sãka

wa mãsu godiya. (3:145)

Yã ku wa ɗanda suka y i ĩmani! Kada ku kasance kamar wa ɗanda suka kãfirta kuma

suka ce wa ´yan´uwansu idan sun yi tafiya a cikin ƙasa kõ kuwa suka kasance a wurin

yãƙi: "Dã sun kasance a wurinmu dã ba su Mutu ba, kuma dã ba a kashe su ba."

(Wannan kuwa) Dõmin Allah Ya sanya wac can magana ta zama nadãma a cikin

zukãtansu. Kuma Allah ne Yake rãyarwa kuma Yake matarwa. Kuma Allah, ga abin

da kuke aikatãwa, Mai gani ne. (3:156)

arci ya yi kama da mutu wa! M ai barci ba ya iya sanin abinda yake gud ãna

lõkacin da yake barci. Lõkacin barci mutum na iya zarcewa yayi babbar mutuwa.

Yazo a cikin Al ƙur‟ani mai girma:

اللَّوُ يػَتػَوَفَّى اْلَْنػْفُسَ حِينَ مَوْتِهَا وَالَّتِي لَمْ تَمُتْ فِي مَنَامِهَا فػَيُمْسِكُ الَّتِي قَضَى عَلَيػْهَا

الْمَوْتَ وَيػُرْسِلُ اْلُْخْرَى إِلَى أَجَلٍ مُسَمِّى إِفَّ فِي ذَلِكَ َلَيَاتٍ لِقَوْـٍ يػَتػَفَكَّرُوفَ

Allah ne ke ka rɓar rãyuka a lõkacin mutuwarsu, da wa ɗannan da ba su mutu ba, a

cikin barcinsu. Sa´an nan Ya riƙe wanda Ya hukunta mutuwa a kansa kuma Ya saki

gudar, har zuwa ga ajali ambatacce. Lalle a cikin wancan, haƙĩƙa, akwai ãyõyi ga

mutãne wa ɗanda ke yin tunãni. (39:42)

Sabõda haka: (Garga ɗi):

Kuma kada lalle ka ce ga wani abu, "Lalle ni, mai aikatãwa ne ga wancan a gõbe."

Fãce (sai kã ce) idan Allah Y ã so. Kuma ka ambaci (sunan) Ubangijinka idan ka

manta, kuma ka ce: "Ɗammãni ga Ubangijĩna, Ya shiryar da ni ga abi n da yake shi ne

mafi kusa ga wannan na shiriya." (18:23 -24). B

7

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 5

اللهم باسمك ربي وضعت جنبي وباسمك أرفعو أف أمسكت نفسي فارحمها وإف

أرسلتها فاحفظها بما تحفظ بو الصالحين من عبادؾ "

Allãhumma bi -ismiKa Rabbiy wada’atu janbiy , wa bismiKa arfa’uhu, in amsakTa

nafsiy farhamhã, wa’in arsaltaha fahfazhã bima Tahfazu bihis sãlihina min ibãdika.

Fassara:

Yã Ubangiji! Da sunanKa na sanya gefena (na sanya b ãyana na kishingi ɗa domin

barci), kuma da sunanKa nake tãshi (nake ɗaga shi - bãyana). Idan Ka riƙe rãyina, to

Ka jiƙansa. Idan kuma Ka aikomin dashi (Ka dãwomin da shi), to Ka kiyãye shi da

irin kiyãyewarKa da Kake kiyãye salihai daga bãyinKa.

(Bukhari da Muslimu suka rawaito, daga Abu Huraira (R.A))

وعَنْ حُذَيػْفَةَ : أَفّ النَّبِيَّ صَلَّى اللَّوُ عَلَيْوِ وَسَلَّمَ كَافَ إِ ذَا أَوَى إِلَى فِرَاشِوِ قَاؿَ : اللَّهُمَّ

بِاسْمِكَ أَحْيَا وَبِاسْمِكَ أَمُوتُ وَإِذَا أَصْبَحَ قَاؿَ : الْحَمْدُ لِلَّوِ الَّذِي أَحْيَانَا بػَعْدَمَا أَمَاتػَنَا

وَإِلَيْوِ النُّشُورُ.

Daga Huzaifa (R.A) : Anna bi (SAW) ya kasance idan zai kwanta yakance: Allãhumma

bismiKa ahyã wa bismiKa amũtu . Idan ya tashi da Asuba, sai yace: Alhamdu lillãhil

laziy ahyãna ba’ada mã amãtana wa ilaihin nushũr .6

ahalar fitar rai ya banbanta daga mutum zuwa mutum, gwalgwadon ts oron

Allah. Akwai wa ɗanda ba‟a sassauta musu , lõkacin da za‟a karfi r ãyinsu,

kamar yadda za a karanta nan gaba ka ɗan in Allah Ya yarda . Amma kãfin fitar rai,

kõwane mai rai zai fuskanci abin da ake kira mãyen mutuwa.

6. Bukhari ya rawaito hadisin. W

8

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 6 õ ã ã ƙã A lkacin da mutum ya kusa mutuwa, k fin mal ’ikan mutuwa ya raso, mutum zai

ã ã ã fra fuskantar wani abu da ake kira m yen mutuwa. Shi dai m yen mutuwa za mu iya

ã õ cewa wata wahalar jinya ce wacce mutumin da zai mutu yake k muwa da ita, l kaci

ɗ ã ã kaan, k fin mal ’ikan mutuwa ya zo.

õ ã ã Wani l kaci, masu jinyar mutum sukan g ne cewar mutum ya shiga m yen mutuwa

ãõ ƙ idan sun ga wassu al mmi kamar yawan shauwa, numfashi sama -sama , ko surutai7.

ũ ã ã ã õ Mminai sukan g ne cewar sun shiga h lin m yen mutuwa, a wannan l kacin ne suke

ɗ ã ã barin wasiyya a wa anda suke kusa da su. Shi m yen mutuwa, ance kowa sai ya k mu

da shi.

õ ã A lkacin jinyar wafatinsa ( Sallall hu alaihi wa sallam ) ya kasance a gabansa akwai

õ ã masaki da ruwa, yana tsma hannayensa yana sh fawa a fuskarsa yana cewa: ãL ilaha

ã illal lah, Tabbas mutu wa tana da m ye! ã A wani hadisi, y ce da Nana Fatima (R.A):

ɗã ã ã ɗ Ya iyta! Cewa shi, ya riga yazo ma B banki abin da Allah b Ya auke ma wani don

ã ƙ waf tin ranar iyama.8

õ ƙ ã ã A lkacin da ajalin Abubakar Siddi (R.A) ya gab to, Nana Aisha (R.A) t karanta

baiti: لعُمرؾ ما يغني الثراءُ عن الفتى إذا حشرجت يوماً وضاؽ بها الصدرُ

Sai ya y ãye fuskarsa yace: Ba haka ba ya Aisha, sai dai cewa nace (fadin Allah (S)) :

وَجَاءتْ سَكْرَةُ الْمَوْتِ بِالْحَقّْ ذَلِكَ مَا كُنتَ مِنْوُ تَحِيدُ

Kuma mãyen mutuwa ya je da gaskiya. Wannan shĩ ne abin da ka kasance daga

gare shi kanã bijirew a. (50:19)

ũ sun bayyana yadda suka An rawaito cewar Annabi Ibrahim da Annabi M sa (A.S) duk

ɗanɗani m ãyen mutuwa. ka ɗan daga misalin wahalar m ãyen mutuwa shine kamar a

tũra reshen bishiyar ƙãya cikin mutum, b ãyan ƙãya ta kãma kowace jijiyar mutum da

kãyan c ikinsa sai a j ãwo reshen zuwa kirjin mutum . Ana jin zãfin m ãyen mutuwa tun

daga dunduniyar sawu har ya zuwa kirji.9

Ana cikin jin mãyen mutuwa sai mal ã‟ikan mutuwa ya zo, daga nan sauran wasiyyar

mai wasiyya tã ƙãre! ã Idan Allah Ya nufi mutum sai ya furta k almar shah da. Allah Ya

sa mu dace.

õ ã õɓ ã ã Wani l kaci mal ’ikan mutuwa yakan z, karan r yi, tare da wassu mal ’iku. To shin

ã õ ã ɓ ã me yake f ruwa a l kacin da mal ’ikan mutuwa yazo kar an r yi?

7. Maganganu marasa ma’ana ko masu sautin d ãmun jama’a .

8. Salsalatis sahiha 1738.

9. Misali daga misalin Amru bn Ass (R.A), a l õkacin da mutuwa ta kus ãto shi.

9

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 7

Malã‟ika n mutuwa - Malã‟ika Azra‟il - yakan ɗauki r ãyuka k õda yaushe. Yakan z ãro

rãyi ne daga jikin mutm har ya cire shi. Z ãfin fitar rai y ã banbanta daga mutum zuwa

mutum, kamar yadda muka sani. Ga misali, idan mun l ũra da r ãgo ƙosasshe da aka

yanka, zamu san cewa fitar rai abu ne mai wahala. Idan k uma muka l ũra da wani

rãgon r ãmamme wanda aka yanka, z ã mu ga cewar kamar bai sh ã wahala s õsai ba,

wajen fitar rai, sab õda ƙarancin shure -shure.

Haka nan banbancin yake ga mutane! Wanda ya ginu da haram, ya ci riba (interest)

cikin k ãsuwancinsa, y ãfi wanda ya rãme, sabõda azumi da sallah , shan az ãba a lõkacin

fitar rai (mutuwa)

Sũ dai mũminai ana kar ɓar rãyukansu suna masu jin d ãɗin rai, suna masu nisha ɗi.

Sannan Mal ã‟ikun dake kar ɓan rayukansu suna ce musu “ Aminci ya tabbata a kanku,

(za) ku shiga Aljanna sab õda abin da kuka kasance kuna aikat ãwa.”

Ka dubi bush ãra irin wannan! Suna rarrashin mutum da aljanna kafin ma ya mutu.

Lalle kabarin mũminai ba sai an tambayi ni‟ ima ba!

الَّذِينَ تػَتػَوَفَّاىُمُ الْمََلَئِكَةُ طَيّْبِينَ يػَقُولُوفَ سََلَـٌ عَلَيْكُمُ ادْخُلُوا الْجَنَّةَ بِمَا كُنْتُمْ تػَعْمَلُوفَ

Waɗanda malã´iku suke kar ɓar rãyukansu sunã mãsu jin dã ɗin rai, malã´ikun sunã

cewa. "Aminci ya tabbata a kanku. Ku shiga Aljanna sabõda abin da kuka kasance

kuna aikatãwa." (16:32)

(Allah Ya na rantsuwa) da Mal ã’iku masu ɗibar r ãyuka (na mũminai ) da sau ƙi a cikin

nishãdi. (79:2)

Gargaɗi:

Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku nemi taimako da haƙuri game da salla. Lalle ne,

Allah Yana tãre da mãsu haƙuri.

Kuma k ada ku ce ga wa ɗanda ake kashewa a ciki n hanyar Allah: "Matattu ne." ôa,

rãyayyu ne, kuma amma bã ku sansancewa. (2:153 -154)

Kuma lalle ne idan aka kashe ku a cikin hanyar Allah, ko kuwa kuka mutu, haƙĩƙa,

gãfara daga Allah da rahama ne mafi alhe ri daga abin da suke tãrãwa. (3:157 -158)

10

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 8

Musulmai s ũne waɗanda suka sallama ga Allah (SWA) kuma suka daidaitu b ãsa haɗa

wani da Allah wajen bauta, kuma basu yin ts ãfi.

قاؿ رسوؿ اهلل صَلَّى اللَّوُ عَلَيْوِ وَسَلَّمَ « المسلم من سلم المسلموف من لسانو

ويده » رواه مسلم

Manzon Allah (SAW) yã ce: Musulmi shine wanda ( ‘yan uwansa10) musulmai suka

kuɓuta daga (c utarwar) harshensa da hannunsa.

Tõ sũ musulmai, idan Mal ã‟iku suka zo ɗaukar ransu, sai suce musu “ Munzo mu ɗauki

ranku sab õda ajalinku y ã zo, amma kada kuji ts õro, kada kuyi ba ƙin ciki. kuma kuyi

bush ãra a ‘yan -uwanku cewa kun ãda wa’adin aljanna - wato ku cika da kalmar

shahãda don susan k ũ „yan aljanna ne - kuma mune maji ɓintanku a cikin rãyuwa r

dũniya .11 kuma a lãhira ma mune z ã mu zama maji ɓintanku har ku shiga aljanna. Kuna

da duk abinda kuke so a cikin aljan na kuma kuna da abin da r ãyukanku suke so. Kun ã

da liy ãfa mai kyau.

Kai! Wannan lallami (rarrãshi) ya isa musulmi yace a ɗau ransa k õ dã yana tunanin

wani abu na dũniya , ballantana12 wanda z ã a masa haka b ã ya taɓa zama mai son

dũniya.

إِفَّ الَّذِينَ قَالُوا رَبػُّنَا اللَّوُ ثُمَّ اسْتػَقَامُوا تػَتػَنػَزَّؿُ عَلَيْهِمُ الْمََلَئِكَةُ أََلَّ تَخَافُوا وََلَ تَحْزَنُوا

وَأَبْشِرُوا بِالْجَنَّةِ الَّتِي كُنْتُمْ تُوعَدُوفَ (ٖٓ ) نَحْنُ أَوْلِيَاؤُكُمْ فِي الْحَيَاةِ الدُّنػْيَا وَفِي اَلْ خِرَةِ

وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَشْتَهِي أَنػْفُسُكُمْ وَلَكُمْ فِيهَا مَا تَدَّعُوفَ (ٖٔ ) نػُزَُلً مِنْ غَفُورٍ رَحِيمٍ

Lalle waɗannan da suka ce: "Ubangjinmu, shĩ ne Allah," sa´an nan suka daidaitu,

malã´iku na sassau ƙa a kansu (a lõkacin sau ƙar ajalinsu sunã ce musu) "Kada ku ji

tsõro, kuma kada ku yi baƙin ciki, kuma ku yi bushãra da Aljanna, wadda kun

kasance anã yi muku wa´adi da ita." "Mũ ne majibintanku a cikin rãyuwar dũniya

da kuma a cikin Lãhira, kuma a cikinta kunã da abin da rãyukanku ke sha´awa ,

kuma kunã da abin da kuke kira (ak ãwo muku) a cikinta. "A kan liyãfa daga Mai

gãfara, Mai jin ƙai." (41:30 -32)

10. Musulmi ɗan uwan musulmi ne, kamar yadda yazo a wani hadisin.

11. (13:11) … لَوُ مُعَقّْبَاتٌ مِنْ بػَيْنِ يَدَيْوِ وَمِنْ خَلْفِوِ يَحْفَظُونَوُ مِنْ أَمْرِ اللَّوِ

12. Hãsali ma , ko “b ã ya kasancewa ma”

11

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 9 Gargadi:

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma rai ya dũbi abin da ya

gabãtar dõmin gõbe, kuma ku bi Allah da taƙawa. lalle Allah, Mai ƙididdigewa ne ga

abin da kuke aikatãwa. Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka manta Allah shi

kuma Ya mantar da su rãyukansu. Waɗannan sũ ne fãsiƙai. (59:18 -19)

أريني جواد مات ىزَل لعلني أرى ماترين أو بخيَل مخلّدا

aɗannan nau‟ ikan mutu wa guda biyu da b ãyaninsu ya gab ãta- wãto mutuwar

mũminai da musulmai - su ne irin mutuwar masu aiki na gari. A dukkaninsu,

ana rarr ãshin wanda zai mutu, sannan ana yi masa bush ãra da makoma mai kyau.

وَقَدْ دَؿَّ عَلَيْوِ حَدِيثُ عُبَادَةَ بْنِ الصَّامِتِ فِي « الصَّحِيحِ » عَنِ النَّبِي صَلَّى اهللُ عَلَيْوِ

وَسَلَّمَ قَاؿَ: « مَنْ أَحَبَّ لِقَاءَ اللَّوِ أَحَبَّ اللَّوُ لِقَاءَهُ وَمَنْ كَرِهَ لِقَاءَ اللَّوِ كَرِهَ اللَّوُ لِقَاءَهُ،

قَالَتْ عَائِشَةُ أَوْ بػَعْضُ أَزْوَاجِوِ: إِنَّا نَكْرَهُ الْمَوْتَ. قَاؿَ: لَيْسَ ذَاؾَ وَلَكِنَّ الْمُؤْمِنَ إِذَا

حَضَرَهُ الْمَوْتُ بُشّْرَ بِرِضْوَافِ اللَّوِ وَكَرَامَتِوِ فػَلَيْسَ شَيْءٌ أَحَبَّ إِلَيْوِ مِمَّا أَمَامَوُ فَأَحَبَّ

لِقَاءَ اللَّوِ وَأَحَبَّ اللَّوُ لِقَاءَهُ، وَإِفَّ الْكَافِرَ إِذَا حُضِرَ بُشّْرَ بِعَذَ ابِ اللَّوِ وَعُقُوبَتِوِ فػَلَيْسَ

شَيْءٌ أَكْرَهُ إِلَيْوِ مِمَّا أَمَامَوُ فَكَرِهَ لِقَاءَ اللَّوِ وَكَرِهَ اهلل لقاءه »

Annabi (SAW) ya ce: Wanda yakeson gamuwa da Allah, Allah Yana son kar ɓan

bãƙuncinsa. Wanda yake ƙin gamuwa da Allah, Allah b ãya son karɓan ba ƙuncinsa.

Nana Aisha (R .A) tace: ai mu (mutane) b ãmã son mutuwa, sai Annabi (SAW) yace:

Ba wancan ba! Sai dai shi mũmini , idan mutuwa tazo masa, za’ayi masa albishir da

yardar Allah da girmamawarSa gareshi, sai ya zama ( mũmini n) bãya son komai sai

abinda ke gabansa (mutuwa), sai Allah Yaso kar ɓan b ãkuncinsa. Amma kãfiri , idan

akazo, za’ayi masa albishir da azabar Allah da u ƙubarSa, sai yazan b ãbu abin ƙi

gareshi irin abinda ke gabansa (mutuwa), ya zam b ãyason ha ɗuwa da Allah, Allah

kuma bã Ya son k arɓan ba ƙuncinsa.

o yãya masu aikata miyagun ayyuka suke tsammanin irin t ãsu mutuwar? Tabbas!

waɗanda ke aikata miy ãgun ayyuka b ã sa tunanin wata wahala lõkacin

mutuwarsu. Suna ganin cewa mutuwar mũminai da fasiƙai duk ɗãya ce. Kaito! Lalle

abinda suke hukunt ãwa ya munana. W

T

12

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 10 أَـْ حَسِبَ الَّذِينَ اجْتػَرَحُوا السَّيّْئَاتِ أَفْ نَجْعَلَهُمْ كَالَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ

سَوَاءً مَحْيَاىُمْ وَمَمَاتػُهُمْ سَاءَ مَا يَحْكُمُوفَ

Kõ wa ɗanda suka yãgi miyãgun ayyuka sunã zaton Mu sanyã su kamar wa ɗanda

suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, su zama daidai ga rãyuwarsu da

mutuwarsu? Abin da suke hukuntãwa yã mũnanã! (45:21)

Garga ɗi:

Ka ce: "Idan Gidan Lãhira ya kasance sabõda ku, a wurin Allah ke ɓe bã da sauran

mutãne ba, to, ku yi gũrin m utuwa, idan kun kasance mãsu gaskiya." (2:94)

Kuma kada ku ci dukiyõyinku a tsakãninku da ƙarya, kuma ku sãdu da ita zuwa ga

mahukunta dõmin ku ci wani yanki daga dũkiyõyin mutãne da zunubi alhãli kuwa kũ,

kuna sane. (2:188)

Shin ɗãyanku nã son cewa wani l ambu ya kasance a gare shi daga dabĩnai da inabõbi´

maremari suna gudãna daga ƙarƙashinsa, yana da, a cikinsa daga kõwane ´ya´yan

itãce, kuma tsũfa ya sãme shi, alhãli kuwa yana da zũriyya masu rauni sai gũguwa

wadda take a cikinta akwai wuta, ta sãme shi, har ta ƙõne? Kamar wancan ne Allah

Yana bayyanãwar ãyõyi a gare ku, tsammãninku kuna tunãni. (2:266)

anzu kuma sai b ãyanin nau‟ikan mutuwar masu aikata miy ãgun ay yuka da masu

shirka alhali su basu san m ã suna shirkar ba sab õda jahilci.

Dukkan wanda zai kira wata halitta lõkacin addu‟arsa domin ta taimakeshi to wannan

ya kasance mushiriki. Kamar mis ãlin masu kiran aljanu, da saka su wani aiki, na raba

mata da miji, da dai sauransu.

Idan Mal ã‟iku suka je kar ɓar rãyukan Mus hirikai, z ã su tambayesu suce musu “ Ina

abubuwan da kuka kasance kuna kira baicin Allah? Cikin firgita, sai suce: “sun ɓace

daga garemu, bama ganinsu.” Kuma suce: “daman mun kasance kafirai.” Daga nan sai

Malã‟ikun su kar ɓi rãyukan su suna masu fisgar r ãyukan da ƙarfi. Wa‟iyazu bill ãhi.

فَمَنْ أَظْلَمُ مِمَّنِ افػْتػَرَى عَلَى اللَّوِ كَذِبًا أَوْ كَذَّبَ بِآيَاتِوِ أُولَئِكَ يػَنَالُهُمْ نَصِيبػُهُمْ مِنَ

الْكِتَابِ حَتَّى إِذَا جَاءَتػْهُمْ رُسُلُنَا يػَتػَوَفػَّوْنػَهُمْ قَالُوا أَيْنَ مَا كُنْتُمْ تَدْعُوفَ مِنْ دُوفِ اللَّوِ

قَالُوا ضَلُّوا عَنَّا وَشَهِدُوا عَلَى أَنػْفُسِهِمْ أَنػَّهُمْ كَانُوا كَافِرِينَ Y

13

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 11 To, wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ƙaryata

game da ãyõyinSa? Wa ɗannan rabonsu daga Littãfi yanã sãmunsu, har a lõkacin da

ManzanninMu suka je musu, sunã kar ɓar rãyukansu, su ce: "Ĩnã abin da kuka

kasance kunã kira, baicin Allah?" (mushirikai) Su ce: "Sun ɓace daga gare mu,

"Kuma su yi shaida a kansu cewa lalle sũ, sun kasance kãfirai." (7:37)

Garga ɗi:

Kada ku bautã wa kõwa f ãce Allah. Lalle ne ni a gare ku mai gargaɗi ne kuma mai

bushãrã daga gare Shi.

Kuma ku nemi gãfara gun Ubangijinku. Sa´an nan ku tũba zuwa gare Shi, Ya jiyar da

ku dãɗi, jiyarwa mai kyau zuwa ga ajali ambatacce, kuma Ya bai wa dukkan

ma´abucin, girma girm ansa. Amma idan kun jũya, to, lalle nĩ, inã tsõron azãbar yini

mai girma a kanku. Zuwa ga Allah makõmarku take, kuma Shĩ a kan kõme Mai ĩkon

yi ne. (11:2 -4)

Kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah. Bãbu abin bautãwa fãce Shi.

Kõwane abu mai halaka ne fãce fuskarSa. Shi ne da hukunci kuma zuwa gareShi ake

mãyar da ku. (28:88)

Kõ wãne ne yake karɓã , kuma ya sanya ku mamãyan ƙasa? Shin akwai wani abin

bautawa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni. (27:62)

Dã zaka gani, lõkacin da Mal ã‟iku suke kar ɓan rãyukan k ãfirai d ã zaka ga mal ã‟ikun

suna dũkan fusk õkin k ãfiran - suna gabza musu mãri - suna dũkan ɗuwãwunsu kuma

suna ce musu “ ku ɗanɗani azabar g õbara: wancan sab õda abinda kuka aikata ne. ”13

فَكَيْفَ إِذَا تػَوَفػَّتػْهُمُ الْمََلَئِكَةُ يَضْرِبُوفَ وُجُوىَهُمْ وَأَدْبَارَىُمْ

To y ãya halinsu yake lõkacin da mal ã’ikun ke kar ɓar rãyukansu, (malã’ikun ) suna

masu d ũkan fusk õkinsu da ɗuwaiwansu? (47:27)

„Yan uwa sai mu l ũra mu gani, h ãlin n ãsu lõkacin mutuwa , sannan muyi garga ɗi ga

makusantanmu.

“Wannan (halin n ãsu), ya kasan ce ne domin lalle su sunbi abin da ya fus ãtar da

Allah kuma (domin) sunƙi yardarSa, sab õda haka Ya ɓãta ayyukansu. (47:28)

13. Bayanin aya ta 50 a suratul Anfal (8:50) .

14

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 12 Garga ɗi:

Ka ce wa waɗanda suka kãfirta, idan sun hanu, zã a gãfarta musu abin da ya ri ga ya

shige, kuma idan sun kõma, to, hanyar kãfiran farko, haƙĩƙa, ta shũɗe. (8:38)

Lalle ne wanɗanda suka kãfirta, kuma suka mutu alhãli kuwa suna kãfirai to bã zã a

karɓi cike da ƙasa na zinãri daga ɗ ãyansu ba, kõ dã ya yi fansa da shi, waɗannan sunã

da azãba mai raɗaɗi, kuma bã su da wasu mataimaka. (3:91)

Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni, sa´an nan kuma suka kãfirta, sa´an nan kuma suka yi

ĩmani, sa´an nan kuma suka kãfirta sa´an nan kuma suka ƙãra kãfirci, Allah bai

kasance Yanã gãfarta musu ba, kuma bã zai shiryar da su ga hanya ba. (4:137)

Kuma kada wa ɗanda suka kãfirta su yi zaton cewa, lalle ne jinkirin da Muke yi musu

alheri ne ga rãyukansu. Munã yi musu jinkirin ne dõmin su ƙãra laifi kawai kuma suna

da azãba mai wulãƙantarwa. (3:178)

A lõkacin da Mal ã‟iku suke kar ɓan rãyukan azzalumai, za su bãsu az ãba wajen kar ɓan

rãyukan, sannan idan hankalin azzaluman ya fita daga jikinsu sabõda mãyen mutuwa,

sai mal ã‟ikun su sh ãƙe wuyan azzaluman suce musu: “ ku fitar rayukanku da kanku . A

yau ana s ãka muku da az ãbar wul ãƙanci sab õda abinda kuka kasance daga ay õyinSa

kuna yin girman kai. ”

Allah madaukakin Sarki Yana cewa:

Kuma wãne ne mafi zãlunci daga wanda ya ƙirƙira ƙarya ga Allah, kõ kuwa ya ce:

"An yi wahayi zuwa gare ni," alhãli kuwa ba a yi wahayin kõme ba zuwa gare shi, da

wanda ya ce: "zan sau ƙar da misãlin abin da Allah Ya sau ƙar?" Kuma dã kã gani, a

lõkacin da azzãlumai suke cikin mãyen mutuwa, kuma malã´iku sunã mãsu shimfiɗa

hannuwansu, (sunã ce musu) "Ku fitar da kanku; a yau anã s ãka muku da azãbar

wulãƙanci sabõda abin da kuka kasance kunã faɗa, wanin gaskiya, ga Allah kuma

kun kasance daga ãyõyinSa kunã yin girman kai." (6:93)

Garga ɗi:

Kuma dã Allah Yanã kãma mutãne da zãluncinsu, dã bai bar wata dabba ba a kan

ƙasa. Kuma amma Y anã jinkirta musu zuwa ga ajali ambatacce. Sa´an nan idan

ajalinsu ya zo, bã zã a yi musu jinkiri ba kõ da sa´a guda, kuma bã zã su gabãta ba.

(16:61)

Bã tũba ba ce ga waɗanda suke aikatãwar mũnanan ayyuka har idan mutuwa ta halarci

ɗãyansu ya ce: "Lalle ne ni, na tũba yanzu, "kuma bã tũba ba ce ga waɗanda suke

mutuwa alhãli kuwa sunã kãfirai, Waɗannan mun yi musu tattalin wata azãba mai

raɗaɗi. (4:18)

15

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 13

Haƙiƙa duk mai s ãɓawa Allah ya kasance mai z ãluntar kansa. Kamar dai masu ci n

dũkiyar mar ãyu da z ãlunci, da masu ƙin fidda zakka kamar yadda Allah (SWA) Yace

a fitar, da masu zina, da masu shan giya da kuma wa ɗanda suke da ikon ƙaura (hijira)

daga kasar da ake z ãlunci sai suka ƙi yin hijira. (ko masu ƙin barin wurin da ake

izgilan ci a ãyoyin Allah)

To waɗannan, banda wanda ya ƙi hijira, idan mal ã‟iku sun zo ɗaukar r ãyukansu, sai

suyi sauri suce wa malã‟ikun, “ba mu kasance muna aikata wani mummunan aiki ba.”

Wai sabõda ko za‟a yi musu sau ƙi wajen kar ɓar rai. Kayya! Lalle ne Allah ne Masani

ga abinda suka kasance suna aikatawa.

الَّذِينَ تػَتػَوَفَّاىُمُ الْمََلَئِكَةُ ظَالِمِي أَنػْفُسِهِمْ فَأَلْقَوُا السَّلَمَ مَا كُنَّا نػَعْمَلُ مِنْ سُوءٍ بػَلَى إِفَّ

اللَّوَ عَلِيمٌ بِمَا كُنْتُمْ تػَعْمَلُوفَ

Waɗanda malã ’iku suke karɓar rãyukansu sunã mãsu zãluntar kansu. Sai suka jefa

neman sulhu (suka ce) "Ba mu kasance muna aikata wani mummũnan aiki ba."

Kayya! Lalle Allah ne Masani ga abin da kuka kasance kunã aikatãwa. (16:28)

Garga ɗi:

"Kuma Shĩ ne wanda Ya sanya ku mãsu maye wa jũna ga ƙasa. Kuma Ya ɗaukaka

sãshenku bisa ga sãshe da darajõji; dõmin Ya jarrabaku a cikin abin da Ya bã ku."

Lalle ne, Ubangijinka Mai gaggãwar uƙũba ne, kuma lalle ne Shi, haƙĩƙa, Mai gãfara

ne, Mai jin ƙai. (6:165)

Sabõda haka, kada dũkiyõyinsu su bã ka sha´awa, ku ma haka ´ya´yansu. Abin sani

kawai, Allah Yanã nufin Ya yi musu azãba, da su a cikin rãyuwar dũniya, kuma

rãyukansu su fita alhãli kuwa sunã kãfirai. (9:55)

u kuma masu z ãluntar kansu wajen ƙin yin hijira, idan malã‟iku sun zo ɗaukar

rãyukansu sai ( malã‟ikun) su tambaye su: “a cikin me kuka kasance?” maimakon

su bada amsar a cikin azzalumai, sai su k ãwo uzuri su ce: “mun kasance wa ɗanda aka

raunana a cikin ƙasa.” Sai malã‟iku suce: “Ashe ƙasar Allah bata kasance

mãyalwaciya ba domin kuyi hijira a cikinta ? Daga zarar sun rasa amsa (ta cewa) sai a

karɓi rãyukansu irin yadda ake kar ɓan rãyin kafirai. Allah Ka kiyaye mu.

Lalle ne, waɗanda malã´ĩku suka karɓi rãyukansu, (alhãli) sunã mãsu zãluntar

kansu, sun ce (musu): "A cikin me kuka kasance?" (Su kuma) suka ce: "Mun kasance

waɗanda aka raunana a cikin ƙasa." Suka ce: "Ashe ƙasar Allah ba ta kasance

mãyalwaciya ba, dõmin ku yi hijira a cikinta?" To, waɗannan makõmarsu

Jahannama ce. Kuma tã mũnana ta zama makõma. (4:97) S

16

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 14 Garga ɗi:

Kuma wanda ya yi hijira a cikin hanyar Allah, zai sãmu, a cikin ƙasa, wurãren jũyãwa

mãsu yawa da yalwa. Kuma wanda ya fita daga gidansa yana mai hijira zuwa ga Allah

da ManzonSa, sa´an nan kuma mutuwa ta riske shi, to, lalle ne, lãdarsa tã auku ga

Allah, Kuma Allah Yã kasance, a gare k u, Mai gãfara, Mai jin ƙai. (4:100)

Yã bãyiNa, waɗanda suka yi ĩmãni! Lalle fa ƙasãTa mai yalwã ce, sabãda haka ku

bauta Mini. Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa ne, sa´an nan zuwa gare Mu ake m ãyar

da ku. (29:56 -57)

قاؿ النبي صلى اهلل عليو وسلم: إنما اْلعماؿ بالنيات، ولكل امرئ ما نوى فمن

كانت ىجرتو إلى اهلل ورسولو، فهجرتو إلى اهلل ورسولو، ومن كانت ىجرتو إلى دنيا

يصيبها، أو امرأة ينكحها، فهجرتو إلى ما ىاجر إليو.

Annabi (SAW) ya ce: ka ɗai dai, ayyuka sai da niyya. Kuma ga Kõwane mutum (ana

hukunci da) abinda ya i niyya. Wanda hijirarsa ta kasance don Allah da ManzonSa

ce, to hijirarsa t ã kasance zuwa ga Allah da ManzonSa. Wanda hijirarsa ta kasance

don dũniya ne, z ãya same ta (ba l ãda). Ko (yayi hijirar don) wata mace da yake

aura, to hijirarsa t ã kasance zuwa ga reshi. 14

Kada a manta : Lalle ne waɗanda suka kãfirta sa´an nan kuma suka kange (mutãne)

daga tafarkin Allah, sa´an nan suka mutu, alhãli kuwa sunã kãfirai, to, Allah bã zai yi

gãfara ba a gare su.15

aɗannan nau‟ikan mutuwa guda shida sune ke faruwa har zuwa tashin ƙiyama.

Idan ka lura, nau‟ika biyu daga cikin shida su muke fata ɗãyansu ya kasance

garemu, amma saura hu ɗun sai dai mu nemi tsari dasu. Sai muyi ƙoƙarin gyara

ayyukanmu domin kowa sai ya ɗanɗana mutuwa. Shin zai kasance wani ya dawwama

alhali mafi kyawun halitta, Annabi Muhammad (SAW) bai kasance ya dawwama a

dũniya ba ba?

( وَمَا جَعَلْنَا لِبَشَرٍ مِنْ قػَبْلِكَ الْخُلْدَ أَفَإِفْ مِتَّ فػَهُمُ الْخَالِدُوفَٖٗ ) كُلُّ نػَفْسٍ ذَائِقَةُ

الْمَوْتِ وَنػَبػْلُوكُمْ بِالشَّرّْ وَالْخَيْرِ فِتػْنَةً وَإِ لَيػْنَا تػُرْجَعُوفَ

“Kuma ba Mu sanya dawwama ga wani mutum ba, a gabãninka. Shin to idan ka

mutu (ya Rasulull ãhi) to sũ ne madawwama? Kõwane rai mai ɗanɗanar mutuwa

ne. Kuma Munã jarraba ku da sharri da alheri dõmin fitina. Kuma zuwa gare Mu ake

mãyar da ku. (21: 34 -35)

14. Daga Baban Hafsa - Umar ɗan ka ɗɗabi (R.A), hadisin annawawi.

15. 47:3 4 W

17

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 15 Garga ɗi:

Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba, A

kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu m ãyar da ku a cikin wata

halitta da ba ku sani ba. (56:60 -61)

Ka ce "Lalle mutuwar nan da kuke gudũ daga g areta,to, lalle ita mai haɗuwa da ku ce

sa´an nan kuma anã m ãyar da kũ zuwa ga masanin fake da bayyane, dõmin Ya bãku

lãbãri game da abin da kuka kasance kunã aikatãwa." (62:8)

Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suka fita daga gidãjensu, alhãli kuwa sũ d ubbai

ne, dõmin tsõron mutuwa? Sai Allah Ya ce musu: "Ku mutu." Sa´an nan kuma Ya

rãyar da su, lalle ne Allah, haƙĩƙa Ma´abũcin falala a kan mutãne ne, kuma amma mafi

yawan mutãne bã su gõdewa. (2:243)

"Inda duk kuka kasance, mutuwa zã ta riske ku, kuma k õ da kun kasance ne a cikin

gãnuwõyi ingãtattu! "Kuma idan wani alheri ya sãme su sai su ce: "Wannan daga

wurin Allah ne," kuma idan wata cũta ta sãme su, sai su ce: "Wannan daga gare ka

ne."Ka ce: "Dukkansu daga Allah ne." To, me ya sãmi waɗannan mutãne, bã su

kusantar fahimtar magana? (4:78)

18

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 16 Daga z ãrar mutum ya mutu, alhali ya san abinda zai tarar, mut ãne zasu shirya

janãzarsa ne kamar yadda shari‟a ta shimfi ɗa. Shi wanda ya mutu irin mutuwa daga

cikin mutuwan nan biyu masu kyau, zai s õ a kai shi kabarinsa da gaggawa, amma

wanda ya mutu irin mutuwar nan ɗãya daga cikin guda huɗu, ba zai s õ a kaishi cikin

azãba ba.

Kabari k õ dã ba‟a b ãda bãyaninsa ba an sani cewar zaiyi z ãfi! Amma fa ga duk wanda

ya mutu yana mai laifi.

Dukkan wanda ya mutu, zai koma cikin kasa ne k õda kuwa a cikin ruwa ya mutu.

Allah (SWA) Yana cewa:

Daga gare ta Muka halitta ku, kuma a cikinta Muke m ãyar da ku, kuma daga gare ta

Muke fitar da ku a wani lõkaci na dabam. (20:55)

A cikin ƙasa ne Allah (SWA) Zai tara mutane har zuwa ranar tashin kiyama, sannan

idan wa‟adin tashin kiyamar yazo sai Allah (SWA) Ya t ãshi kowa kamar dai bai zama

ƙasã ba!

Allah, bãbu abin bautawa face Shi. Lalle ne haƙĩƙa Yana tãra ku har zuwa ga Yinin

Ƙiyãma bãb u shakka a cikinsa. Kuma wãne ne mafi gaskiya daga Allah ga lãbãri.

(4:87)

وقَاؿَ النَّبِيُّ صلى اهلل عليو وسلم:"الْقَبػْرُ رَوْضَةٌ مِنْ رِيَاضِ الْجَنَّةِ، أَوْ حُفْرَةٌ مِنْ حُفَرِ النَّارِ"

Annabi (SAW) yace: kabari dausayi ne daga dausa yen aljanna, ko rãmi daga

rãmukan wuta.

A lõkacin da Malã‟iku n rahama suka tafi da rũhin mũmini , bãyan mutuwarsa,

malã‟iku n da suke sãsannin sama za suji ƙamshi kamar al‟miski, sai suce: “ ƙamshi (ko

iska) mai da ɗi, rũhi mai kyau daga ƙasa (dũniya ) ya zo. Rũhin ba zai wuce wata ƙofa

ba face sai an bu ɗe masa, haka wani Malã‟ika face sai ya masa salati, har sai anje

dashi zuwa wajen Mai Rahama (Mai girma da ɗaukaka). Sannan sai a umarci Mik ã‟ila

(A.S) ya sanya wannan rũhi cikin rayukan mũminai , sannan a rubuta shi a cikin littafin

illiyyun, sannan a maida shi kabarinsa b ãyan an faɗaɗa shi. Malã‟iku biyu (Munkaru

da Nakir) za su zo su tambaye shi ya bada amsa daidai, sannan sai a bu ɗe masa

19

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 17 ƙofofin aljanna yayi ta shan ƙamshi, sannan a haska masa kabarinsa ya zam a kamar

hasken rana. Kyakkyawan aikinsa yana zuwa masa da fuska mai kyau da shigar tuf ãfi

masu kyau, ya t ãya shi hira.

Amma rũhin mai laifi, b ãyan ya mutu, malã‟iku n sama za suce: Rũhi marar kyau ya zo

daga ƙasa (dũniya). Ba za‟a bu ɗe masa ƙofar sama ba: Lalle ne waɗanda suka ƙaryatã

game da ãyõyinMu, kuma suka yi girman kai daga barinsu, bã zã a bubbuɗe musu

kõfõfin sama ba, kuma bã su shiga Aljanna sai (in zai yiwu) raƙumi ya shiga kafar

allũra, kuma kamar wannan ne Muke sãka wa mãsu laifi. (7:40)

Sai a r ubuta rũhin a cikin littafin sijjin, sannan mal ã‟ikan az ãba yai ƙasa dashi yana

hankaɗã shi har zuwa kabarinsa. Malã‟iku biyu zasu tambaye shi ya kasa bada amsa

daidai, sai a bu ɗe masa ƙõfõfin wutar jahannama zafi yana shigo masa. Za a m ãtse

kabarinsa, cik in duhu, mummunan aikinsa zai zo masa hira da mafi m ũnin fuska da

tufãfi.

Allah Ya kiy ãye mu da ga azãbar kabari. kabari dausayi ne daga dausayen aljanna, ko

rãmi daga rãmukan wuta.

وَاعْتَصِمُوا بِحَبْلِ اهللِ جَمِيعاً وََل تػَفَرَّقُوا وَاذْكُرُوا نِعْمَتَ اهللِ عَلَيْكُمْ إِذْ كُنْتُمْ أَعْدَاءً

فَأَلفَ بػَيْنَ قػُلُوبِكُمْ فَأَصْبَحْتُمْ بِنِعْمَتِوِ إِخْوَاناً وَكُنْتُمْ عَلَى شَفَا حُفْرَةٍ مِنَ النَّارِ فَأَنػْقَذَكُمْ

مِنػْهَا كَذَلِكَ يػُبػَيّْنُ اهللُ لَكُمْ آيَاتِوِ لَعَلكُمْ تػَهْتَدُوفَ

Kuma ku yi daid ami da igiyar Allah gabã ɗãya, kuma kada ku rarraba. Kuma ku tuna

ni´imar Allah a kanku a lõkacin da kuka kasance maƙiya sai Ya sanya sõyayya a

tsakãnin zukãtanku sabõda haka kuka wãyi gari, da ni´imarSa, ´yan´uwa. Kuma kun

kasance a kan gã ɓar rãmi na wutã sai Ya tsãmar da ku daga gare ta. Kamar wannan

ne Allah Yake bayyana muku ayõyinSa, tsammãninku, zã ku shiryu. (3:103)

Garga ɗi:

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku jiɓinci waɗansu mutãne da Allah Ya yi hushi a

kansu. Lalle sun yanke tsammãni daga (rahamar ) Lãhira, kamar yadda kãfirai suka

yanke tsammãni daga mazõwa kaburbura. (60:13)

Yã kũ wa ɗanda suka yi ĩmãni! Ku nĩsanci abu mai yãwa na zato. Lalle sãshen zato

laifi ne. Kuma kada ku yi rahõto, kuma kada sãshenku yã yi gulmar sãshe. Shin,

ɗãyanku nã son y aci naman ɗan´uwansa yanã matacce? To, kun ƙĩ shi (cin nãman).

Kuma ku bi Allah da taƙawa. Lalle Allah Mai kar ɓar tũba ne, Mai jin ƙai. (49:12)

Ubangijinku ne Mafi sani ga abinda yake a cikin rãyukanku. Idan kun kasance sãlihai

to lalle ne shĩ Y ã kasance ga mãsu kõmawa gare Shi, Mai gãfara. (17:25)

20

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 18 Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma rai ya dũ bi abin da ya

gabãtar dõmin gõbe, kuma ku bi Allah da taƙawa. lalle Allah, Mai ƙididdigewa ne ga

abin da kuke aikatãwa. Kuma kada ku kasance kamar waɗanda suka manta Allah shi

kuma Ya mantar da su rãyukansu. Waɗannan sũ ne fãsiƙai. (59:18 -19)

( أَفَبِهَذَا الْحَدِيثِ أَنػْتُمْ مُدْىِنُوفَٔٛ ) وَتَجْعَلُوفَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذّْبُوفَ (ٕٛ )

Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa? Kuma ku nã sanya arzikinku

(game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)? (56:81 -82)

( كََلَّ إِذَا بػَلَغَتِ التػَّرَاقِيَٕٙ ) وَقِيلَ مَنْ رَاؽٍ (ٕٚ ) وَظَنَّ أَنَّوُ الْفِرَاؽُ (ٕٛ )

A´aha! idan (rai) ya kai ga karankarmai. kuma aka ce: "Wãne ne mai tawada?"

Kuma ya tab bata cewa rabuwa dai ce. (75:26 -28)

( حَتَّى إِذَا جَاءَ أَحَدَىُمُ الْمَوْتُ قَاؿَ رَبّْ ارْجِعُوفِٜٜ ) لَعَلّْي أَعْمَلُ صَالِحًا فِيمَا تػَرَكْتُ

كََلَّ إِنػَّهَا كَلِمَةٌ ىُوَ قَائِلُهَا وَمِنْ وَرَائِهِمْ بػَرْزَخٌ إِلَى يػَوْـِ يػُبػْعَثُوفَ

Har idan mutuw a ta je wa ɗ ãyansu, sai ya ce: "Yã Ubangijina, Ku m ãyar da ni

(dũniya)." "Tsammãnina in aikata aiki na ƙwarai cikin abinda na bari." Kayya! Lalle

ne ita kalma ce, shĩ ne mafaɗinta, alhãli kuwa a bãya gare su (b ãyan sun mutu)

akwai barzahu har rãnar da zã a tãyar da su. (23:99 -100)

( فػَلَوَْلَ إِذَا بػَلَغَتِ الْحُلْقُوـَٖٛ ) وَأَنػْتُمْ حِينَئِذٍ تػَنْظُرُوفَ (ٗٛ ) وَنَحْنُ أَقػْرَبُ إِلَيْوِ مِنْكُمْ

وَلَكِنْ َلَ تػُبْصِرُوفَ (٘ٛ ) فػَلَوَْلَ إِفْ كُنْتُمْ غَيػْرَ مَدِينِينَ (ٙٛ ) تػَرْجِعُونػَهَا إِفْ كُنْتُمْ

صَادِقِ ينَ (ٚٛ ) فَأَمَّا إِفْ كَافَ مِنَ الْمُقَرَّبِينَ (ٛٛ ) فػَرَوْحٌ وَرَيْحَافٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ (ٜٛ )

وَأَمَّا إِفْ كَافَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ (ٜٓ ) فَسََلَـٌ لَكَ مِنْ أَصْحَابِ الْيَمِينِ (ٜٔ ) وَأَمَّا

إِفْ كَافَ مِنَ الْمُكَذّْبِينَ الضَّالّْينَ (ٕٜ ) فػَنػُزُؿٌ مِنْ حَمِيمٍ (ٖٜ ) وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ (ٜٗ )

إِفَّ ىَذَا لَهُوَ حَقُّ الْيَقِينِ (ٜ٘ ) فَسَبّْحْ بِاسْمِ رَبّْكَ الْعَظِيمِ (ٜٙ )

21

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 19 To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa). Alhãli kuwa kũ, a lõkacin

nan, kunã kallo. Kuma Mũ ne mafi ku santa gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã

ku gani. To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba? Ku

mãyar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya.

To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta, Sai hũtawa da

kyakkyawan abinci da Aljannar ni´ima. Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa

dãma, Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma. Kuma amma

idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun, Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi. Da

ƙõnuwa da Jahĩm, (56:83-94)

رَبػَّنَا إِنػَّنَا سَمِعْنَا مُنَادِيًا يػُنَادِي لِْلِْيمَافِ أَفْ آمِنُوا بِرَبّْكُمْ فَآمَنَّا، رَبػَّنَا فَاغْفِرْ لَنَا ذُنُوبػَنَا

وَكَفّْرْ عَنَّا سَيّْئَاتِنَا وَتػَوَفػَّنَا مَعَ اْلَْبػْرَارِ،

رَبػَّنَا اغْفِرْ لَنَا وَِلِِخْوَانِنَا الَّذِ ينَ سَبػَقُونَا بِاِلِْيمَافِ وََلَ تَجْعَلْ فِي قػُلُوبِنَا غَِلِّ لِلَّذِينَ آمَنُوا

رَبػَّنَا إِنَّكَ رَءُوؼٌ رَحِيمٌ،

Rabbana innana sami‟ina mun ãdiyan yun ãdiy lil iymãni an ãminũ bi Rabbikum fa

ãmanna, Rabban ã fag‟fir lan ã zunũbana wa kaffir ann ã sayyi‟ ãtina wa tawaffan ã ma‟al

abrar. (3:193)

Rabbanag‟fir lan ã wa li‟ik -wãninal laziyna sabak ũna bil iymãni, wala taj‟al fi y

ƙulũbina gillal lil laziyna ãmanũ, Rabban ã innaKa Ra‟ ũfur Rahim. (59:10)

FASSARA:

"Yã Ubangijinmu! Lalle ne mũ mun ji Mai kira yanã kira zuwa ga ĩmãni cewa: “Ku yi

ĩmãni da Ubangijinku”, Sai muka yi ĩmãni. Yã Ubangijinmu! Sabõda haka Ka gãfarta

mana zunubanmu, kuma Ka kankare miyãgun ayyukanmu daga gare mu. Kuma Ka

karɓi rãyukanmu tãre da mutãnen kirki. (3:193)

…"Yã Ubangijinmu! Ka yi gãf ara a gare mu, kuma ga ´yan´uwanmu, waɗanda suka

riga mu yin ĩmãni, kada Ka sanya wani ƙulli a cikin zukãtanmu ga waɗanda suka yi

ĩmãni. Yã Ubangijinmu! Lalle Kai ne Mai tausayi, Mai jin ƙai. (59:10)

22

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 20

Tashin dũniya shine r ãnar da Malã‟ika Isrãfil zai busa ƙaho kowa ya mutu, banda

wanɗanda Allah Ya so. Ance sune Malã‟iku hudu: Jibrilu, Mik ã‟ilu, Isr ãfilu da

Azrã‟ilu (Mal ã‟ikan mutuwa)

Da yawan mutane, sab õda sun karanta al ãmõmin da za su zo kafin t ãshin dũniya , suna

ganin suna da sauran lõkaci da za su tuba su k õma ga Allah (SWA) daga zarar sun ga

wata babbar alamar t ãshin dũniya . Kaito! Lõkacin da ãya (alãma) ke bayyana wanda

bai yi imãni ba tun farko b ã zai iya yin imãni ba.

Shin, sunã jiran (wani abu), fãce dai mal ã´iku su je musu kõ kuwa Ubangijinka Ya je,

kõ kuwa sãshen ãyõyin Ubangijinka ya je. A rãnar da sãshen ãyõyin Ubangijinka

yake zuwa, ĩmãnin rai wanda bai kasance yã yi ĩmãnin ba a gabãni, kõ kuwa ya yi

tsiwirwirin wani alheri, bã ya amfãninsa. Ka ce: "Ku y i jira: Lalle ne mũ, mãsu jira

ne. (6:158)

Garga ɗi:

Ka haƙurtar da ranka tãre da waɗanda ke kiran Ubangijinsu, sãfe da maraice, sunã

nufin yardarSa. Kuma kada idãnunka su jũya daga barinsu, kanã nufin ƙawar rãyuwar

dũniya. Kuma kada ka bi wanda Muka shagal tar da zũciyarsa daga hukuncinMu, kuma

ya bi son zuciyarsa, alhãli kuwa al´amarinsa ya kasance yin ɓarna. (18:28)

Wanda Allah Ya ɓatar to bãbu mai shiryarwa a gare shi: kuma Yanã barin su, a cikin

ɓatarsu sunã ɗimuwa. (7:186)

ada ka kasance daga cikin mutane masu tamb ãyar “yaushe ne dũniya za ta

tashi?” abin da ake so kawai shine garga ɗi ga mutane cewa “t ãshin dũniya yayi

kusa!” Tamb ãyar lõkacin da zata tashi kamar neman ƙaryata lõkacin ne.

بَلْ يُرِيدُ اِلِْنْسَافُ لِيػَفْجُرَ أَمَامَوُ. يَسْأَؿُ أَيَّافَ يػَوْـُ الْقِيَامَةِ (75:5 -6)

( إِنَّمَا أَنْتَ مُنْذِرُ مَنْ يَخْشَاىَا٘ٗ ) كَأَنػَّهُمْ يػَوْـَ يػَرَوْنػَهَا لَمْ يػَلْبَثُوا إَِلَّ عَشِيَّةً أَوْ ضُحَاىَا

(79:45 -46)

K

23

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 21 Ba haka ba! Mutum so yake, ya yi fãjirci, ya ƙaryata abin da yake a gabansa. Yanã

tamb ãya: "Yaushe ne Rãnar Ƙiyãma?" (75:5 -6)

Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta. Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su

zauna ba fãce a lõkacin marħce ko hantsinsa. (79:45 -46)

Mutane (mushirikai) suna ganin cewa akwai sauran shekaru masu yawa k ãfin a t ãshi

dũniya ! Har yanzu ba su ga wassu manyan ãyõyi na al ãmar t ãshin dũniya ba.

Allah maɗaukakin Sarki Ya ce:

Lalle ne su, sunã ganinta ( ƙiyama) mai nĩsa. Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa. (70:6 -)

Garga ɗi:

Kuma dã Allah Yana gaggãwa ga mutãne da sharri kamar yadda Yake gaggauta musu

da alheri, haƙĩƙa dã an hukunta ajalinsu zuwa gare su. Sabõda haka Munã barin

waɗanda ba su ƙaunar gamuwa da Mu a cikin kangararsu sunã ta ɗimuwa. (10:11)

Lalle ne waɗanda suke bã su yin ĩmãni da Lãhira, Mun ƙawãta musu ayyukansu,

sabõda haka sunã ɗimuwa. (27:4)

Kuma suka ce: "Ya Ubangijinmu! Ka gaggauta mana da rabonmu (na az ãba), a

gabãnin rãnar bincike. (38:16)

رَبػَّنَا َلَ تُزِغْ قػُلُوبػَنَا بػَعْدَ إِذْ ىَدَيػْتػَنَا وَىَبْ لَنَا مِنْ لَدُنْكَ رَحْمَةً إِنَّكَ أَنْتَ الْوَىَّابُ ( ٛ)

رَبػَّنَا إِنَّكَ جَامِعُ النَّاسِ لِيػَوْـٍ َلَ رَيْبَ فِيوِ إِفَّ اللَّوَ َلَ يُخْلِفُ الْمِيعَادَ (ٜ )

Rabbana lã tuzig ƙulũbana ba’ada iz hadaitana wa hab’lan ã min ladunKa rahmah.

InnaKa anTal Wahhab. Rabban ã innaKa jãmi’un nãsa li yaumil lã -raiba fihi,

innallãha lã yukliful miy’ãd.

Yã Ubangijinmu! Kada Ka karkatar da zukãtanmu bãyan har Kã shiryar da mu, kuma

Ka bã mu rahama daga gunKa. Lalle ne, Kai, Kai ne Mai yawan kyauta.

"Yã Ubangijimu! Lalle ne Kai, Mai tãra mutãne ne dõmin wani yini w anda bãbu

shakka a gare shi, Lalle ne Allah bã Ya sãɓãwar lõkacin al ƙawari." (3:8-9)

24

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 22

Garga ɗi:

Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku ci ku sha daga mãsu dãɗin abin da Muka azurta ku.

Kuma ku gõde wa Allah, idan kun kasance Shi kuke bauta wa.

Kawai abin da Ya h aramta a kanku, mũshe da Jini da nãman alade da abin da aka

kurũrũta game da shi ga wanin Allah. To, wanda aka matsã, wanin ɗan tãwãye, kuma

banda mai zãlunci, to bãbu laifi a kansa. Lalle ne Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai.

(2:172 -173)

Yã ku mutãne! Ku ci daga abin da yake a cikin ƙasa, wanda yake halal, mai dãɗi.

Kuma kada ku bi zambiyõyin Shaiɗan. Lalle ne shi, gare ku, maƙiyi ne bayyananne.

Yana umurnin ku ne kawai da mugun aiki da alfãsha, kuma da ku faɗi abin da baku

sani ba ga Allah. (2:168 -169)

Kuma lalle ne, Muna jarrabar ku da wani abu daga tsõro da yunwa da naƙasa daga

dũkiya da rãyuka da ´ya´yan itãce. Kuma ka yi bishãra ga mãsu haƙuri. Waɗanda suke

idan wata masĩfa ta sãme su, sai su ce: Inn ã lillãhi wa inn ã ilaihi r ãji‟un - "Lalle ne mũ

ga Allah muke, kuma lalle ne mũ, zuwa gare Shi, muke kõmãwa." (2:155 -156)

haruddan sa‟a fa sun riga sun zo! Shin mai mutane suke jira ne?

To shin sunã jiran (wani abu)? Fãce Sa´a ta je musu bisa abke (ba shiri), dõmin

lalle sharuɗɗanta sun zo. To, yãya tunãw arsu take, idan har ta je musu?

(47:18)

Garga ɗi:

Lalle abin da ake yi muku al ƙawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne. Kuma lalle

sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne. (51:5 -6)

aɗai dai waɗanda ba su yin imãni da ranar al ƙiyama, sune suke neman gaggawar

zuwan sa‟a, suke ƙidayi -faɗi ga shekarar da sa‟a zata ts ãya. Allah ne Wanda Ya

saukar da Littãfi da gaskiya, da sikeli. Kuma me ya sanar da kai (cewa anã)

tsammãnin Sa´ar kusa take? (42:17)

Garga ɗi:

Makusanciya (alkiyama) fa, tã yi kusa. Bãbu wan i rai, banda Allah, mai iya bãyani

gare ta. (53:57 -58)

(To) Shin, lõkaci bai yi ba ne, ga waɗanda suka yi ĩmãnĩ, zukãtansu su yi tawãlu´i ga

ambaton Allah da abin da ya sau ƙa daga gaskiya? Kada su kasance kamar waɗanda S

K

25

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 23 aka bai wa littãf i a gabãnin haka, sa i zãmani ya yi tsawo a kansu, sabõda haka

zukãtansu suka ƙeƙashe, kuma masu yawa daga cikinsu fãsiƙai ne.

Ku sani cewa Allah Yanã rãyar da ƙasã (ma) bãyan mutuwarta. Lalle Mun bayyana

muku ãyõyi da fatan zã ku yi hankali. (57:16 -17)

isabin mutane fa, ya kusanta! Mutane sun shagala. Ba‟a maganar komai sai

yadda za‟a gyara dũniya kafin wassu shekar ũ masu zuwa. Allah (SWA) Y ana

cewa:

Hisãbin mutãne ya kusanta gare su, alhãli kuwa (mutanen) sunã a cikin gafala, sunã

mãsu bijirewa. (21:1 -2)

Garga ɗi:

A´aha! Bã haka ba, kunã son mai gaugawar nan ne ( dũniya), Kunã barin ta ƙarshen

(Lãhira). (75: 20 -21)

l‟amarin af‟kuwar sa‟a y ã kasance kamar kiftawar ido, kai! Y ã fi kiftawar ido

sauri16.

…sabõda haka kada rãyuwar dũniya ta rũ ɗar da ku, kuma kada marũ ɗi ya

rũɗe ku game da Allah. (35:5)

Lalle wa ɗanda suka yi zalunci, suka ƙaryata game da ranar gamuwa da Allah, sunyi

hasara…(6:31)

16. Duba aya 16:77 H

A

26

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 24

Kafin bũsar ƙaho ta farko, b ũsar da kowa zai mutu, akwai wassu abubuwa da za su

faru anan dũniya , waɗannan abubuwa kuwa sune alãmõmin tashin dũniya .

Kamar yadda yawancin mutane sun san alãmõmin tãshin dũniya , ba sai anyi b ayãni

mai tsawo ba.

Yãjũju da m ãjũju wassu halitttu ne masu tsawon ƙafa goma sha hu ɗu waɗanda suk e

yin barna a cikin ƙasa lõkacin Zulƙarnaini.

A lõkacin da Zulƙarnaini ya gina katangar karfe ya t õshe yadda suke shigowa suyi

ɓarna sai yace: “ wannan rahama ne daga Ubangijina, amma idan wa’adi ya yi,

katangar zata karye guntu -guntu sannan su shigo suyi ba rna.”

Katangar ance an gina ta ne a ƙarni na goma sha biyar. Daga gininta har zuwa rãyuwa r

Annabi Muhammad (SAW) shekaru ɗari shida da sittin da hu ɗu (664) kenan *.

Annabi Muhammad (SAW) ya ce: “ Lã ilaha illal l ãh! B one ga L ãrabãwa daga wani

sharri da yai kusa! Yau, an bu ɗe Katangar Y ãjuju da M ãjuju misãlin haka”17 (tsawon

tsakãnin babban yatsa da yatsan nuni)”

Har sa´ad da aka bũ ɗe Yãjũju da Mãjũju alhãli kuwa sunã gaggãwa daga kõwane

tudun ƙasa. Kuma wa´adin nan tabbatacce y ã kusanto, (idan t ãshin hanka lin yazo)

sai gã ta idãnun waɗanda suka kãfirta sunã bayyanannu, (sunã cewa), "Yã

kaitonmu! Haƙĩƙa mun kasance a cikin gafala daga wannan! ôa, mun kasance dai

mãsu zãlunci!" (21:96 -97)

Garga ɗi:

Kuma kada ka kasance daga waɗanda suke ƙaryatãwa game da ãyõ yin Allah, har ka

kasance daga mãsu hasãra. Kuma waɗanda suka ƙaryata game da ãyõyinMu, zã Mu yi

musu istidrãji daga inda ba su sani ba. (7:182)

Lalle ne, wannan wata tunãtarwa ce, sai dai wanda ya so, ya kãma hanyar ƙwarai zuwa

ga Ubangijinsa. (73:19)

17. Muttafa ƙun alaihi, Daga Zainab bnt Jahash (R.A)

27

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 25

Wannan dabbar ana kiranta Jassasa. Ance „yar t ãguwar Annabi S ãlihu (A .S) ce. Za ta

fito daga d ũtsen safa, na garin Makka, da hantsi. Za ta fito tana ri ƙe da sandar Annabi

Mũsa (A .S) da h ãtimin Annabi Sulaiman (A .S) ta ce wa mutane ba sa yin ĩmãni n

gaskiya. Ance dabbar za ta fito ne sau uku. Allah dai Shi ne mafi sani.

وَإِذَا وَقَعَ الْقَوْؿُ عَلَيْهِمْ أَخْرَجْنَا لَهُمْ دَابَّةً مِنَ اْلَْرْضِ تُكَلّْمُهُمْ أَفَّ النَّاسَ كَانُوا بِآيَاتِنَا َلَ يُوقِنُوفَ

Kuma idan magana ta auku a kansu, Munã fitar musu da wata dabba daga ƙasa,

tanã yi musu magana, cewa "Lalle mutãne sun kasance game da ãyõyi nMu, ba su

yin ĩmãnin yaƙĩni." (27:82)

Garga ɗi:

Yã ku waɗanda suka yi ĩmani! Ku shiga cikin Musulunci gabã ɗ ãya; kuma kada ku bi

zambiyõyin Shaiɗan; lalle ne shĩ a gare ku maƙiyi ne, bayyananne. To, idan kun

karkace daga b ãyan hujjõji bayyanannu sun zo muku to ku sani cewa lalle ne Allah,

Mabuwãyi ne, Mai hikima. (2:208 -209)

Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! wanda ya yi ridda daga gare ku daga addi ninSa, to,

Allah zai zo da wasu mutãne, Yanã son su kuma sunã son Sa, mãsu tawãlu´i a kan

mũminai mãsu izza a kan kãfirai. Sunã yin, jihãdi a cikin hanyar Allah, kuma bã su

tsõron zargin wani mai zargi. Waccan falalar Allah ce, Yanã bãyar da ita ga wanda

Yake so. Kuma Allah M ayalwaci ne, Mai ilmi. (5:54)

قُلِ اللَّهُمَّ مَالِكَ الْمُلْكِ تػُؤْتِي الْمُلْكَ مَنْ تَشَاءُ وَتػَنْزِعُ الْمُلْكَ مِمَّنْ تَشَاءُ وَتُعِزُّ مَنْ

تَشَاءُ وَتُذِؿُّ مَنْ تَشَاءُ بِيَدِؾَ الْخَيػْرُ إِنَّكَ عَلَى كُلّْ شَيْءٍ قَدِ يرٌ. تُولِجُ اللَّيْلَ فِي النػَّهَارِ

وَتُولِجُ النػَّهَارَ فِي اللَّيْلِ وَتُخْرِجُ الْحَيَّ مِنَ الْمَيّْتِ وَتُخْرِجُ الْمَيّْتَ مِنَ الْحَيّْ وَتػَرْزُؽُ مَنْ

تَشَاءُ بِغَيْرِ حِسَابٍ .

ƙulil-lãhumma m ãlikal mulki, t ũtil mulka man tash ã’u, wa tanzi’ul mu lka miman

tash ã’. Wa tu’izzu man tash ã’u wa tuzillu man tash ã’. bi yadiKal khair, innaKa ala

kulli shai’in ƙadiyr.

Tũlijul laila fin nah ãri wa t ũlijun nah ãra fil layl, wa tuk hrijul hayya minal mayyiti wa

tukhrijul mayyita minal hayyi, wa tarzu ƙu man Tash ã’u bi gairi hisab. (3:26 -27)

28

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 26 Gargadi:

Allah ne Yake shimfiɗa arziki ga wanda Yake so, kuma Yanã ƙuntatãwa. Kuma sun yi

farin ciki da rãyuwar dũniya, alhali kuwa rãyuwar dũniya ba ta zama ba dangane ga ta

Lãhira fãce jin dãɗi kaɗan. Kuma Waɗanda suka kãfirta , sunã cewa, "Don me ba a

sauƙar da wata ãyã ba a kansa daga Ubangijinsa?" Ka ce: "Lalle ne Allah Yanã ɓatar

da wanda Yake so kuma Yanã shiryar da wanda ya tũba zuwa gare shi." (3:26 -27)

A lõkacin da za‟a rufe ƙofar tũbã, sama za ta tsage (kamar yadda take ts ãgewa, wal ƙiya

ta fito ta haska gari) ta fitar da wani jan haske wanda zai rufeta duka. Wallahu a‟alamu

A lõkacin da sama za tayi ja, imãni n wanda baiyi imãni ba tun farko, ba zai amfane shi

ba.18 Gã rãnar nan tafe, Kõ yau k õ gõbe! A ranar za ka iya g ãne masu laifi da wata

alãma, haka kuma za ka iya g ãne masu ĩmãni da al ãmarsu.

( فَإِذَا انْشَقَّتِ السَّمَاءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَالدّْىَافِٖٚ ) فَبِأَيّْ آَلَءِ رَبّْكُمَا تُكَذّْبَافِ (ٖٛ )

فػَيػَوْمَئِذٍ َلَ يُسْأَؿُ عَنْ ذَنْبِوِ إِنْسٌ وََلَ جَافّّ (ٜٖ ) فَبِأَيّْ آَلَءِ رَبّْكُمَا تُكَذّْبَافِ (ٓٗ )

يػُعْرَؼُ الْمُجْرِمُوفَ بِسِيمَاىُمْ فػَيػُؤْخَذُ بِالنػَّوَاصِي وَاْلَْقْدَاـِ (ٔٗ )

Sa´an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta. To, sabõda wanne

daga ni´imõmin Ubangijin ku, kuke ƙaryatãwa?

To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani. To, sabõda

wanne daga ni´imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?

zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwark waɗarsu da

sãwãyensu. (55:37 -41)

Gargaɗi:

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne

Mafi sani ga mãsu shiryuwa. Sabõda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa. Sunã fatar ka

sassauta, su kuma sũ sassauta. Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

Mai zunɗe, mai yãwo da gulma. Mai hana alheri mai zãlunci, mai zunubi. Mai girman

kai, bãyan haka kuma la´ĩ mi (bã ya son alheri). Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne." Zã Mu

yi masa al ãma a kan hanci. (68:7 -16)

18. Duba aya 6:158 .

29

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 27

Babu wani Annabi da ya zo face sai da yayi garga ɗi a mutane nsa game da Dujjal.19

Shi dai Dujjal ya kasance mai ido ɗãya. An rubuta, a fuskarsa, harrufan kafun da fa‟un

da ra‟un, a rarrabe (wato ma‟ana kãfiri ). Duk mũmini zai gani, kuma zai iya karantãwa

ko bai iya rubũtu ba.20

Dujjal zai fito ne , yace shi Ubangijin halittu ne, tare dashi akwai ruwa, akwai kuma

wuta a d ãya gefen. Shi ruwan nan wuta ce a ɓoye. Wutar kuma ruwan sanyi ne. a

lõkacin masu son zuciya zasu z aɓi ruwansa. Allah Ya kiyashe mu !

Kafin Dujjal ya bayyana sai an mance da garga ɗin ambatonsa,21 kuma sai ɗumãmar

dũniya ( Global warming ) yã kai maƙura, ya zama kamar 80% na bishiyõyi sun ƙõne,22

kai! Tarihin Dujjal zai ɗauki lõkaci da wuri (space) mai yawa a cikin wannan littafi,

sabõda haka ne ba zan samu d ãmar rubũta shi duka ba. Za‟a iya duba Sahihul Muslim -

Kitãbul fitni wa ashr ãɗus sa’a da sauran littattafai dõmin ƙarin b ãyani.

Dujjal dai yakan fitini mutane, daga ƙarshe a kashe shi a wajen garin Madina.

Garga ɗi:

Kuma kamar wannan ne Muke bayyana ãyõyi, daki -daki, kuma dõmin hanyar mãsu

laifi ta bayyana. (6:55)

Idan Allah Ya taimake ku, to, bãbu marinjayi a gare ku. Kuma idan Ya yarɓe ku, to,

wãne ne wanda yake taimakon ku bãyanSa? Kuma ga Allah sai mũmi nai su dõgara.

(3:160)

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Idan kun yi tafiya (a cikin ƙasa), dõmin jihãdi, to, ku

nemi bãyani. Kuma kada ku ce wa wanda ya jĩfa sallama zuwa gare ku: "Bã Musulmi

kake ba." Kunã neman hãjar rãyuwar dũniya, to, a wurin Allah akwai ganimõmi mãsu

yawa. Kamar wannan ne kuka kasance a gabãnin ku musulunta, sa´an nan Allah Ya yi

muku falala. Sabõda haka ku zan neman bayãni. Lalle ne Allah Yã kasance, ga abin da

kuke aikatãwa, Masani. (4:94)

Bãyan Dujjal ya fito, yayi arba‟in a cikin ƙasa, sai Allah (SWA) Ya sau ƙar da Annabi

Isã (A.S). Annabi Is ã (A.S) zai nemi Dujjal ya kashe shi.

Mutane za su zauna, cikin zaman l ãfiya, ba wani t ãshin hankali tsakanin mutum biyu,

tsawon shekaru bakwai. Sannan sai Alla h (SWA) Ya aiko da wata iska mai sanyi daga

yankin garin Sham. Wannan iskar da zarar mai ɗigon imãni a zuciya ya she ƙe ta, sai

19. Bukhari ya rawaito, hadisi daga Ibn Umar (R.A) . A Bible Dujjal suke kira AntiChrist (False messiah )

20. Siffofin jikin Dujjal, Littafin Nihayatal lam shafi na 230. Ã

21. Hadisi daga R ãshid bn Sa’ad, ruwayar Abdullahi bn Ahmad daga riwayar Ba ƙiyya daga Safwan bn Amru

22. Hadisin ya ambaci raguwar ruwan sama da ƙonewar tsirrai. daga Um ãmatu al Bahiliy, ruwayar Muslim.

30

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 28 mutuwa! Dũniya zãta zama cike da marasa ilmi a wannan lõkacin , ba su san umarni ba

haka kuma hani. Zina zata yawaita…

Garga ɗi:

Bai zama addini ba dõmin kun jũyar da fuskõkinku wajen gabas da yamma, kuma

amma addini shi ne ga wanda ya yi ĩmãni da Allah da Rãnar Lãhira da malã´iku da

Littattafan sama da Annabãwa, kuma ya bãyar da dũkiya, akan yana son ta, ga mai

zumunta da marãyu da matalauta da ɗan hanya da mãsu rõƙo, kuma a cikin fansar

wuya, kuma ya ts ãyar da salla, kuma ya bãyar da zakka, da mãsu cika alkawari idan

sun ƙulla alkawarin da mãsu haƙuri a cikin tsanani da cũta da lõkacin yãƙi. Waɗannan

su ne suka yi gaskiya. Kuma waɗannan su ne mãsu taƙawa. (2:177)

23

Kafin sã‟a ta ts ãya, sai y ã kasance birnin Rum (Ingila da Amirka) ya kece yawan

lãrabãwa, y ã kasance mafi yawan ƙidaya (population) a duniya.24 To anan ne Dujjal

zai fito, kuma kisan mutane (terrorism ) zai yawaita yay in fitowar ta Dujjal.

قاؿ المستورد القرشي عند عمرو بن العاص سمعت رسوؿ اهلل صلى اهلل عليو وسلم يقوؿ:

تقوـ الساعة والروـ أكثر الناس فقاؿ عمرو أبصر ما تقوؿ قاؿ أقوؿ ما سمعت من رسوؿ

اهلل صلى اهلل عليو وسلم قاؿ لئن قلت ذاؾ إف فيهم لخصاَلً أربعاً : إنهم ْلسرع الناس كرة ً

بعد فرة ، وإنهم لخير الناس لمسكينٍ و فقير وضعيف، وإنهم ْلحلم الناس عند فتنة ،

وأوشكهم ٍوخير ىم و الربعة حسنة ًجميلة ً وإنهم ْلمنع الناس من ظلم الملوؾ (رواه المسلم )

Masturadu ya fa ɗa a wajen Amru bnl As (R.A): Nã ji Manzon Allah (SAW) yana cewa:

Sa’a zata tsaya, Rũmawa su suka fi yawan mutane . Sai Amru bnl As yace: kayi bĩtar

abinda kake fa ɗi! Sai yace masa ina fa ɗan abinda naji Manzon Allah (SAW) ya fa ɗã ne.

Sai Amru bnl As yace: To in anyi la’akari da hadĩsin da ka fa ɗa, lalle zã su zama suna

da wa ɗannan halãye guda hu ɗu:

1. Sune mutane, a ƙwaryar du niya, masu gaggawar binciken raunin su.

2. Su kasance masu kirki a miskĩnai da faƙĩrai da raunãnã (misãlin US AID).

3. Su kasance mutane masu tunanin fitina.

4. Na hu ɗu, mai kyau, mai ƙ ãyatarwa, suna hana mulkin danniya.

23. Rumawa sune turawan Europe da America. Sun samu s ũnan Rum daga Asfar bn Rum bn Isu –qurɗabi

24. Duba Sahihul Muslim - Kitabul Fitna: B ãbu ta ƙumus S ã’a war Rum ak’tharan n ãsi.

31

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 29

Garga ɗi:

A. L . M .

An rinjãyi Rũmawa. A cik in mafi kusantar ƙasarsu, kuma sũ, a bãyan rinjãyarsu, zã su

rinjãya. A cikin ´yan shekaru. Al´amari na Allah ne a gabãnin kõme da bãyansa, kuma

a rãnar nan mũminai zã su yi farin ciki. Da taimakon Allah Yanã taimakon wanda

Yake so. Kuma Shĩ ne Mabuwãyi, M ai jin ƙai. Wa´adin Allah, Allah bã ya sãɓãwa ga

wa´adinsa, kuma amma mafi yawan mutãne ba su sani ba. Sunã sanin bayyanannar

rãyuwar dũniya, alhãli kuwa sũ shagalallu ne daga rãyuwar Lãhira. (30:1 -7)

Wannan yana daga cikin alãmõmi manya na t ãshin dũniya . Rãna z ã tayi kusufi

(kisfewa) sau uku. Ɗãya daga Gabas, ɗãya a yamma, ɗãya kuma a ƙasar L ãrabãwa.

ƙarshen wa ɗannan kus ũfai, rana zata fit õ ta yamma s ãɓanin yadda ta s ãba ta gabas.

عن أبي ىريرة أنو قاؿ: ثَلث إذا خرجن َلينفع نفسا إيمانها لم تكن آمنت

من قبل أو كسبت في إيمانها خيرا: طلوع الشمس من مغربها، والدجاؿ، ودابة

اْلرض.

Daga Abu Huraira (R.A) ya ce Manzon Allah (SAW) ya ce: Guda uku, idan suka fito

ĩmãnin rai wanda bai kasance yã yi ĩmãnin ba a gabãni, kõ ku wa ya yi tsiwirwirin

wani alheri, bã ya amfãninsa.25 Fitowar rana ta wajen faduwarta, da Dujjal da

Dabba mai magana. (Mus limu ya rawaito)

Garga ɗi:

Kuma ga Allah gaibin sammai da ƙasa yake. Kuma zuwa gareShi ake m ãyar da

dukkan al´amari. Sabõda haka ku bauta Masa kuma ku dõgara a kanSa. Kuma

Ubangijinka bai zama Mai gafala daga abin da kuke aikatãwa ba. (11:123)

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, mushirikai najasa ne, sabõda haka

kada su kusanci Masallaci Mai alfarma a bãyan shekararsu wannan. Kum a idan kun ji

tsõron talauci to, da sannu Allah zai wadãta ku daga falalarSa, idan Ya so. Lalle Allah

ne Masani, M ai hikima. (9:28)

Shin kõ kun amince cewa W anda ke cikin sama, bã zai iya shãfe ƙasa tãre da ku ba,

sai ga ta tana m ai girgiza? Kõ kun amince cewa W anda ke cikin sama bã zai iya sako

muku iskar gũguwa ba? To, zã ku san yadda (ãƙibar) gargaɗiNa take. (67:16 -17)

25. Daga ãyar 6:158

32

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 30

Wannan yana daga cikin manyan al ãmõmin t ãshin dũniya, ance ita ce al ãma ta karshe

(Allah dai Shi n e Mafi sani). W ata wuta ce za ta fito daga ƙasar Yaman (Yemen) ta

kõra mutane zuwa wurin da za‟a tattarasu d õmin t ãshin dũniya. Wassu malamai sunce

Baitul Ma ƙadisi ne wurin da za‟a tara mutane d õmin t ãshin dũniya sabõda kasancewar

sa mafi kusa da sama. Wa ɗannan b ãyanai suna cikin Sahihul Muslim da tafsirin S ãwi.

Wassu sunce wata farar ƙasã ce madaida iciya, marar wata al ãma ficecciya da wani

mutum ya sani. (Allah dai Shi ne Mafi sani).

عن حذيفة بن أسيد قاؿ: أشرؼ علينا رسوؿ اهلل من غرفة فقاؿ: ماذا تذكروف ؟

قلنا: نتذاكر الساعة قاؿ: فإنها َل تقوـ حتى يكوف قبلها عشر آيات: الدجاؿ،

والدخاف، والدابة، وطلوع الشمس من مغربها، ويأجوج ومأجوج، ونزوؿ عيس ى بن

مريم عليو السَلـ، وثَلثة خسوؼ: خسف بالمشرؽ، وخسف بالمغرب، وخسف

بجزيرة العرب، وآخر ذلك نار تخرج من أر ض اليمن تطرد الناس إلى محشرىم.

Garga ɗi:

Kuma bãbu wata dabba a cikin ƙasa kuma bãbu wani tsuntsu wanda yake t ãshi da

fukafukinsa fãce al´umma ne misãlanku. Ba Mu yi sakacin barin kõme ba a cikin

Littãfi, sa´an nan kuma zuwa ga Ubangijinsu ake tãra su.

Kuma waɗanda su ka ƙaryata game da ãyõyinMu, kurãme ne kuma bebãye, a cikin

duffai. Wanda Allah Ya so Yanã ɓatar da shi, kuma wanda Ya so zai sanya shi a kan

hanya madaidaiciya.

Ka ce: "Shĩn, kun gan ku, idan azãbar Allah ta zo muku, kõ Sã´ar Tashin Kiyãma ta zo

muku, shi n wanin Allah kuke kira, idan dai kun kasance mãsu gaskiya?"

"ôa, Shĩ dai kuke kira sai Ya kuranye abin da kuke kira zuwa gare Shi, idan Ya so,

kuma kunã mantãwar abin da kuke yin shirkin tãre da shi." (6:38 -41)

Hayaƙ i daga sama zai lullu ɓe dũniya, ko wani sãshenta. Mafi yawan Mãlamai sun tafi

akan cewa sh ĩ wannan hayãki na alãmar tãshin dũniya bai bayyana ba tukun, kuma zai

bayyana ne kusa da tashin dũniya. Akan wannan ilmi Aliyu bn Abi ɗãlib da Ibn Abbas

da Abũ Sa‟ ĩdul khudriy (R.A) suka tafi. Daga cikin hadisan da ke nuni da bayyanar

hayãki a ƙarshen dũniya sun ha ɗa da hadisin Huzaifa, wanda yake wannan shãfin.

33

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 31

Duk da cewa Abdullahi Ibn Mas‟ud da jama‟ar salaf ãwa da yawa sun tafi akan cewa

wannan hay ãki ya bayyana a lokacin Manzon Allah (SAW), a ta ƙaice dai, magana

mafi rinj ãye ita ce: wannan hay ãƙin yana daga ay õyin da ake jira, wa ɗanda basu f ãru

ba. Kuma ana fahimtar wannan ne daga fa ɗin Allah (SWA):

( فَارْتَقِبْ يػَوْـَ تَأْتِي السَّمَاءُ بِدُخَافٍ مُبِينٍٓٔ ) يػَغْشَ ى النَّاسَ ىَذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ

Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã t a zo da hayãƙi bayyananne. Yanã rufe

mutãne. Wannan wata azãba ce mai ra ɗaɗi. (44:10 -11)

Garga ɗi:

Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne. Inã tunãwa take a

gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da garga ɗin saukar

azãbar, ba su kar ɓa ba)? Sa´an nan suka jũya baya daga gare shi, Ku ma suka ce:

"Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci." Lalle Mũ, Mãsu kuranyewar azãba ne, a ɗan

lõkaci ka ɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin). Rãnar da Muke damƙa, damƙa

mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne. (44:12 -16)

Dũniya ba za ta t ãshi ba har sai wahala tayi yawa yadda za a samu mutum yana

sha‟awar na cikin kabari , yana cewa: “kaito! In ãma na kasance ni ne a cikin wannan

kabarin.”26 Waɗannan mutanen basu da addini face bala‟i.

A yau mutane da yawa sukan kashe kansu sabõda wahala , ko su ce “in ã ma sun mutu

sun hũta”, to yãya hãlin mutanen gobe?

قاؿ ابن مسعود سيأتي عليكم زماف لو وجد أحدكم الموت يباع َلشتراه .27

Ibn Mas’ud (R.A) ya ce: Da sannu zamani zai zo muku, da dayanku zai samu ana

sayar da mutuwa, da ya saya!

وىذا العيش ما َل خير فيو ... أَل موت يباع فأشتريو

Garga ɗi:

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa´a kamar mãsu laifi? Me ya sãme ku, yãya

kuke yin hukunci (da haka)? Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke

karantãwa? Cewã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abinda rãyukanku suka zãɓa? Kõ kunã

(riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãn ar Ƙiyãma, cewa lalle

26. Muttafakun alaihi, daga Abu Huraira (R.A)

27. Daga Littafin Alamatis Sa’at as -Sugra na Yahya bn Musa Zahraniy, Imam Jami Kabir, Garin Tabuka.

34

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 32 ne kunã da abin da kuke hukuntãwa kanku? Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke

lãmunc ewã ga sãmun wannan (hukuncin)? Kõ sunã da abõkan tãrewa (ga wannan

ra´ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya. (68:35 -

41)

Alãmõmin t ãshin dũniya da aka karanta, in banda na ƙarshe, suna daga cikin manyan

alãmõmin t ãshin dũniya. Da yawan ƙanãnan al ãmõmin t ãshin dũniya sun f ãru. Yawan

ƙanãnan al ãmõmin t ãshin dũniya yafi y ãwan manyan. Sab õda haka za a samu bĩtar

jerin sũnayensu a ƙarshen wannan littafin in Allah (SWA) Ya yarda.

وَإِنَّوُ لَعِلْمٌ لِلسَّاعَةِ فََلَ تَمْتػَرُفَّ بِهَا وَاتَّبِعُوفِ ىَذَا صِرَاطٌ مُسْتَقِيمٌ

Kuma lalle shĩ, haƙĩƙa, wani ilmi ne na Sa´a, sabõda haka, kada ku yi shakka a

gare ta, k uma ku bĩ Ni. Wannan ita ce hanya madaidaiciya.

Garga ɗi:

Shin, ba ka gani ba, zuwa ga waɗanda suke riyãwar cewa sunã ĩmãni da abin da aka

sauƙar zuwa gare ka da abin da aka sau ƙar daga gabãninka, sunã nufin su kai ƙãra

zuwa ga Ɗãgũtu alhãli kuwa, lalle ne , an umurce su da su kãfirta da shi, kuma Shaiɗan

yanã neman ya ɓatar da su, ɓatarwa mai nĩsa. Kuma idan aka ce musu: "Ku zo zuwa

ga abin da Allah Ya saukar, kuma zuwa ga Manzo" zã ka ga munãfukai sunã kange

mutãne daga gare ka, kangewa. To, y ãya, idan wat a masĩfa ta sãme su, sabõda abin da

hannuwansu suka gabãtar sa´an nan kuma su je maka sunã rantsuwa da Allah cewa,

"Ba mu yi nufin kõme ba sai kyautatawa da daidaitãwa."? Waɗannan ne waɗanda

Allah Ya san abin da ke cikin zukãtansu. Sabõda haka ka kau da ka i daga gare su,

kuma ka yi musu gargaɗi, kuma ka g ãya musu, a cikin sha´anin kansu, magana mai

nauyi da fasãha. (4:60 -63)

Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙ aryata wannan lãbãri . Zã Mu yi musu istidrãji daga

inda ba su sani ba. Ina jinkirtã musu (ne), lalle kai diNa mai ƙarfi ne. (68:44 -45)

( رَبػَّنَا َلَ تُزِغْ قػُلُوبػَنَا بػَعْدَ إِذْ ىَدَيػْتػَنَا وَىَبْ لَنَا مِنْ لَدُنْكَ رَحْمَةً إِنَّكَ أَنْتَ الْوَىَّابُٛ )

رَبػَّنَا إِنَّكَ جَامِعُ النَّاسِ لِيػَوْـٍ َلَ رَيْبَ فِيوِ إِفَّ اللَّوَ َلَ يُخْلِفُ الْمِيعَ ادَ (ٜ)

35

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 33

A lõkacin da sa‟a za ta tsãya, za‟a umarci Malã‟ika Azrafil (A .S) ya bũsa ƙaho. Idan

wannan Malã‟ika n ya busa ƙahon, Kõwane abu mai rai zai mutu, illa m ã shã Allah.

Sannan idan aka umarce shi da ya s ãke bũsawa, Kõwane macec ce zai tashi domin yayi

bayãnin abubuwan da ya aikata a dũniya . Ga b ãyaninsu kamar haka:

Innã lillãhi wa inn ã ilaihi r ãji‟un! Idan wa‟adi ya cika, Allah (SWA) Ya umarci

Malã‟ika n bũsar ƙaho da ya busa, idan Malã‟ika n ya bũsa ƙahon, duk kan mai rai da

yake sama da mai rai da yake ƙasa za su firgita, sannan k õwa zai mutu face wanda

Allah Ya so ba za su mutu a wannan b ũsar ba, Sune Malã‟iku huɗu masu daraja

(Jibril, Mik ã‟il, Isr ãfil da Malã‟ika n mutuwa). Wannan b ũsar kuwa za ta biyo b ãyan

fitõwar dabba mai magana ne , ko fitõwar rana ta wurinda take fa ɗuwa. Allah (SWA)

Shi ne mafi sani, kuma Yana cewa:

وَيػَوْـَ يػُنػْفَخُ فِي الصُّورِ فػَفَزِعَ مَنْ فِي السَّمَاوَاتِ وَمَنْ فِي اْلَْرْضِ إَِلَّ مَنْ شَاءَ اللَّوُ

وَكُلّّ أَتػَوْهُ دَاخِرِينَ

Kum a a rãnar da ake bũsa a cikin ƙaho, sai wand ã yake a cikin sammai da waɗanda

suke a cikin ƙasa su firgita, fãce wanda Allah Ya so, kuma du kkansu, su je Masa

sunã ƙasƙantattu. (27:87)

Garga ɗi:

Ashe, ba Mu sanya ƙasa matattarã ba. Ga rãyayyu da matattu, (77:25-26)

Shin, mutum yana zaton cewa bã zã Mu tãra ƙasusuwansa ba? Na´am! Mãsu ĩkon yi

Muke a kan Mu daidaita gaɓõɓin yãtsunsa. (75:3 -4)

Ka ce: "Shĩn, kun gan ku, idan azãbar Allah ta zo muku, kõ Sã´ar Tashin Kiyãma ta zo

muku, shin wanin Allah kuke kira, idan dai kun kasance mãsu gaskiya?" "ôa, Shĩ dai

kuke kira sai Ya kuranye abin da kuke kira zuwa gare Shi, idan Ya so, kuma kunã

mantãwar abin da kuke yin shirkin tãre da shi." (6:40 -41)

Ga Allah (SWA) mulki yake a ranar da ake busa a cikin ƙaho. ( 6:73)

Daga zarar b ũsar ƙaho tayi arba‟in (Allah Shine mafi sani), to sai busa ta biyu ta biyo

bãya.

Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa. Mai biyar ta (bũsa ta biyu)

nã biye. (79:6 -7)

36

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 34

A lõkacin da kowa ke mace, za‟a na ɗe sama kamar yadda ka sani ake na ɗe takarda ko

tãbarma. Kamar dai yadda aka fara halittar sama alh ãli mutum bai kasance k õmai ba,

kuma bai san yadda yake ba, haka nan za‟a m aida halittar sama a lõkacin da mutum

bai san yadda ya ke ba. Allah Mai ik o! Allah (SWA) Y ana cewa:

A rãnar da Muke naɗe s ama kamar n aɗewar takarda ga abũbuwan rubũtãwa ,

kamar yadda Muka fãra a far kon halitta Muke mãyar da ita. Wa´adi ne a Kanmu.

Lalle ne Mun kasance Mãsu aikatãwa. (21:104)

Garga ɗi:

Ka ce: "Ku dũbi abin da yake cikin sammai da ƙasa."Kuma ãyõyi da garga ɗi bã su

wadãtarwa ga mutãne wa ɗanda bã su yin ĩmãni (10:101)

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba, Da abin da bã ku iya g ani. Lalle

ne, shi (Alƙur´ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne. (69:38 -40)

Lalle ne shi (Alƙur´ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai. Ga wanda ya so, daga

cikinku, ya shiryu. (81:27 -28)

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai. Kuma lalle, ne shi

gaskiya ce ta yaƙini. Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma. (69:50 )

Kuma ka yi hukunci a tsakãninsu da abin da Allah Ya sau ƙar kuma kada ka bĩbiyi son

zũciyõyinsu, kuma ka yi saunar su fitine ka daga sãshen abin da Allah Ya saukar zuwa

gare ka. To, idan sun juya bãya, to, ka sani cewa, kawai Allah yana nufin Ya sãme su

da masĩfa ne sabõda sãshen zunubansu. Kuma lalle ne, mãsu yawa daga mutãne,

haƙĩƙa, fãsiƙai ne. (5:49 -50)

Duwatsu za su zama kamar girgije, suna tafiya suna narkewa, suna malãlã kamar

tudun rai rãyi. Ana she ƙe duw ãtsu sheƙewa, kafin kace wani abu wurin da duwatsun

suka kasance ya zama fa ƙo. (56:4 -6)

Rãnar da ƙasa ke raurawa, da duwãtsu , kuma duwãtsu su kasance tudun rai rãyi mai

malãlã. (73:14)

37

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 35 Kuma sunã tamb ãyarka daga duwãtsu, sai ka ce: "Ubangijina Yana sheƙe su

sheƙewa, Sa´an nan Yanã b arin (wurinsu) faƙo mai santsi. (20:105 -106)

Garga ɗi:

Kuma kanã ganin duwãtsu, kanã zaton su sandararru, alhãli kuwa sũ sunã shũɗewa

shũɗew ar girgije, bisa sanã´ar Allah W anda Ya kyautata kõwane abu. Lalle Shi, Mai

lãbartãwa ne game da abin da kuke aikatãwa. (27:88)

Kuma kada ku yi ɓarna a cikin ƙasa a bãyan gyaranta. Kuma ku kirãye Shi (Allah)

sabõda tsõro da tsammãni ;28 lalle ne rahama r Allah makusanciya ce daga mãsu

kyautatãwa. (7:56)

Wannan ƙasar da muke kai, b ã akanta ne za‟a yi his ãbi ba. Za‟a yi his ãbi ne akan wata

farar ƙasa, wacce ba‟a ta ɓa amfani da ita wajen n õma ba, ko wata alf ãsha ba.

A lõkacin da aka ni ƙe duwa tsu aka ha ɗasu da ƙasa, aka daidaita tudu da kwari, sai a

naɗe ƙasa. Za‟a kawo wata ƙasa, fara mai kyau, a shimfi ɗa. Akan wannan farar kasar

ne za‟a yi his ãbi ga kõwane mutum da aljani.

يػَوْـَ تػُبَدَّؿُ اْلَْرْضُ غَيػْرَ اْلَْرْضِ وَالسَّمَاوَاتُ وَبػَرَزُوا لِلَّوِ الْوَاحِدِ الْقَهَّارِ

A rãnar da ake musanya ƙasa bã ƙasar nan ba, da sammai kuma su bayyana ga

Allah Maka ɗaici, Mai tanƙwasãwa. (14:48)

lõkacin da za a canza ƙasa, ance ma‟ab õta kaburbura suna kan sir ãɗi. Sirãɗi

wata hanya ce s ĩririya, akan wutar Jahannnama. Ba makawa ga kõwane mutum,

sai ya hau kan sira ɗi! Shin lõkacin canza ƙasa ne kawai mutane za su hau kan sira ɗi?

Allah Shi ne mafi sani. Abin da Ya sanar damu kawai:

وَإِفْ مِنْكُمْ إَِلَّ وَارِدُىَا كَافَ عَلَى رَبّْكَ حَتْمًا مَقْضِيِّا

Kuma bãbu kõwa daga gare ku sai mai tuzga mata. Yã kasance wajibi ga

Ubangijinka, hukuntacce. (19:71)

Garga ɗi:

Yã kũ mutãne! Ku tuna ni´imar Allah a kanku. Shin, akwai wani mai halitta wanin

Allah da zai azurta ku daga sama da, ƙasã? Bãbu wani abin bautãwa , fãce Shi. To,

yãya ake karkatar da ku? (35:3)

28. Kar ku ƙira wani waliyyi. A

38

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 36 To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗãya. Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma

aka niƙa su niƙãwa ɗãya. A ran nan, mai aukuwa zã ta auku. (69:13 -15)

ta dai bũsa ta biyu, ta k asance wata tsawa ce guda ɗãya, wacce zata t ãyar da

Kõwane macecce daga barcinsa.

Tõ, ita kam, tsãwa ce guda kawai. Sai kawai gã su (halittu) a bãyan ƙasa. (79:13 -14)

aƙiƙa bũsar ƙaho ta biyu tafi ta farko firgitarwa. Sautin b ũsa ta biyu ya sha

banban da na b ãsa ta farko. Ka tuna cewa b ũsa ta farko an busa wa r ãyayyu ne

domin su mutu, amma b ũsa ta biyu, za‟a bũsa wa matattu ne d õmin su t ãshi su bada

bayãni game da abinda suka aikata a dũniya . Sannan a yi hukunci a tsak ãninsu da

gaskiya, a s ãka wa Kõwane rai da mafi alherin abin da ya aikata.

Garga ɗi:

Kuma sunã ce wa, "Yaushe wannan hukunci yake aukuwa idan kun kasance mãsu

gaskiya?" Ka ce: "Ranar hukuncin nan, ĩmãnin waɗanda suka kãfirta bã zai amfãne su

ba (a cikinta) kuma bã zã a yi musu jinkiri ba." Sa bõda haka ka kau da kai daga

barinsu, kuma, ka yi jira lalle, sũ ma mãsu jira ne. (32:28 -30)

Sabõda haka, ka bar su! Rãnar da mai kiran zai yi kira zuwa ga wani abu abin ƙyama.

Ƙasƙantattu ga idanunsu zã su fito daga kaburburansu, kamar dai sũ fãri ne waɗa nda

suka wãtse. Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cewa, "Wannan yini

ne mai wuya!" (54:6 -8)

aga z ãrar anyi b ũsa, bũsa ta biyu, Allah (SWA) Z ai umarci ƙasa ta kece ta jefar

da kõwane abin da yake cikinta. ƙasa z ã ta saur ãri maganar Ubang ijinta. Annabi

Muhammadu (SAW) shi ne wanda zai fara fita daga cikin kabarinsa .29 ƙasa za ta

wãtsar da sauran mutane ta w õfinta daga komai.30

29. وعن أنس قاؿ سمعت رسوؿ اهلل صلى اهلل عليو وسلم يقوؿ اني َلوؿ الناس تشق اَلرض عن

جمجمتي يوـ القيامة...(السنن الكبرى)

30. Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta, Kuma ta jefar da abin da yake a ci kinta, ta wõfinta daga kõme. Kuma ta

saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren, (84:3 -5)

Rãnar da ƙasã ke tsattsãgewa daga gare su, sunã mãsu gaggãwa. Wancan tãrãwar mutãne ne, mai sauƙi a

gare Mu. (50:44) I

H

D

39

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 37 Garga ɗi:

Abin sani kawai, wa ɗanda suke saur ãre ne suke kar ɓãwa, kuma matattu Allah Yake

tãyar da su, Sa´an nan kuma zuwa gare Shi ake m ãyar da su. (6:36)

Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku kasance tãre da mãsu

gaskiya. (9:119)

Daga zarar mut ãne sun fito daga kaburbura da gagg ãwa, za su nufi wajen Malã‟ika n

da yake b ũsa ƙaho ƙungiya -ƙungiya .31 Kafirai za su ce: kai! Wannan yini da wahala

yake!

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata

kafaffiyar (t ũta), suke yin gaugãwa. Ma ƙasƙanta ga id ãnunsu, wani wala ƙanci yana

rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi mus a alkawari (a kansa).

(70:43 -44)

Sunã gaggãwar tafiya zuwa ga mai kiran, kãfirai na cewa, "Wannan yini ne mai

wuya!" (54:8)

Garga ɗi:

Mene ne ya yi jinsu, kuma mene ne ya yi ganinsu a rãnar da suke zo Mana! Amma

azzãlumai sunã a cikin ɓata bayyananna. Ku ma kayi musu gargaɗi da rãnar nadãma a

lõkacin da aka hukunta al´a mari alhãli kuwa sunã a cikin ɓa ta, kuma sũ bã su yin

ĩmãni. (19:38 -39)

ãshin mut ãne da fitarsu daga kaburbura lõkacin bũsa ta biyu ya banbanta a

tsakãninsu bisa ga ta ƙawarsu. Wassu za su tãshi a firgice, wassu kuma kamar

wanda ya farka daga barci - ya tãshi ya zauna sannan ya t ãshi tsaye…

31. Duba ayar 78:18. T

40

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 38

Dukkan mũminai , masu ta ƙawa, s ãlihai da dukkan wa ɗanda suka aikata ayyukan

ƙwarai, za su tãshi daga kabari ba tare da wata firgita ba. Kuma ba sa tare da ba ƙin

ciki daɗa ko wani dã nã sani.

Daga zarar sun t ãshi, sai malã‟iku su zo suyi musu mar ãba suce musu: “wannan

yininku ne wanda kuka kasance ana yi muku wa‟adi da shi.

Firgitar nan mafi girm a, bã zã ta baƙantã musu rai ba. Kuma malã´iku na yi musu

marãba (sunã cewa) "Wannan yininku ne wanda kuka kasance anã yi muku wa´adi

da shi." (21:103)

Garga ɗi:

Wanda ya zo da kyakkyawan aiki guda, to, yanã da mafi alheri daga gare shi. Kuma sũ

daga wata f irgita, a yinin nan, amintattu ne. Kuma wanda ya zo da m ũgun aiki, to (ka

ƙaddara) , an kife fuskõkinsu a cikin wuta. Ko (kuna tsammanin) zã a sãka muku, fãce

da abin da kuka kasance ku nã aikatãwa? (27:89 -90)

Dukkan masu shirka ta hanyar amfani da aljannu ko wata shirkar ta daban , za su t ãshi

daga kabari, a cikin firgita. Daga z ãrar sun tuna masu taimakonsu a dũniya kuma suka

ga masu taimakon n ãsu a cikin wani h ãli na has ãra, sai suyi shiru, su kasa magana.

Daga nan sai s u nemi gujewa abo kan shirkar tã su don sabõda kar su k ãwo musu wani

uzuri. Allah (SWA) Yana cewa:

Kuma a rãnar da sa´a ke tsayuwa, mãsu laifi zã su kãsa magana. Kuma bã su da

masu ceto daga abũbuwan shirkinsu, kuma sun kasance mãsu kãfircewa daga

abũbuwan shirkinsu. (30:12 -13)

Nau‟ikan shirka ya ha ɗa da ts ãfi, rufa ido, b õkanci, ƙulle-kullen raba mas õya, riya da

dai sauransu.

Garga ɗi:

Ka ce: "Godiya ta tabbata ga Allah, kuma aminci ya tabbata bisa ga bãyinSa, waɗanda

Ya zãɓa." Shin Allah ne Mafi alheri ko abin da suke yin sh irki da Shi?

41

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 39 Kõ wãne ne Ya halitta sammai da ƙasa kuma Ya sau ƙar muku, daga, sama, wani ruwa,

Muka tsirar, game da shi, gõnaki mãsu sha´awa, (wa ɗanda) ba ya kasancewa gare ku,

ku tsirar da itãcensu? Shin, akwai abin bautãwa tãre da Allah? ô a, sũ mutãne ne suna

daidaitãwa (r Allah da wani).

Kõ kuwa wãne ne Ya sanya ƙasa tabbatacciya, kuma Ya sanya kõguna a tsakãninta

kuma Ya sanya mata manyan duwãtsu tabbatattu, kuma Ya sanya wani shãmaki32 a

tsakãnin tekuna biyu? Shin akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? ôa, mafi

yawansu ba su sanĩ ba.

Kõ wãne ne yake karɓãwa na cikin ƙaƙa-nikãyi (addu‟a), kuma ya sanya ku mamãyan

ƙasa? Shin akwai wani abin baut ãwa tãre da Allah? Kaɗan ƙwarai kuke yin tunãni.

Kõ wãne ne yake shiryarwa a cikin duffan ƙasa da teku, kuma wãne ne Yake aikõwar

iskõki dõmin bãyar da bushãra a gaba ga rahamarSa? Ashe akwai wani abin bautãwa

tãre da Allah? tsarki yã tabbata ga Allah daga barin abin da suke shirki da Shi.

Kõ wãne ne yake fãra halitta sa´an nan kuma ya m ãyar da ita, kuma w ãne ne Ya

arzurta ku daga sama da ƙasa? Ashe, akwai wani abin bautãwa tãre da Allah? Ka ce:

"Ku kãwo dalĩlinku idan kun kasance mãsu gaskiya."

Ka ce: "Bãbu wanda ya san gaibi a cikin sammai da ƙasa fãce Allah. Kuma bã su

sansancewar a yaushe ne zã a tãyar da su." ôa, saninsu ya kai a cikin Lãhira ôa,

sunã cikin shakka daga gare ta. ôa, sũ daga gare ta makãfin zũci ne.

Kuma waɗanda suka kãfirta suka ce: "Shin idan mun kasance turɓ ãya, mu da

ubanninmu, shin, haƙĩƙa, waɗanda ake fitarwa ne?" "Lalle ne, haƙĩƙa, an yi mana

wa´adi ga wannan, mũ da ubanninmu, daga gabãnin haka. Wannan bã kõme ba ne fãce

tãtsũniyõyin farko."

Ka ce: "Ku yi tafiya a c ikin ƙasa, sa´an nan ku dũba, ya ya ãƙibar mãsu laifi take?"

(27:59 -69)

Musulmai wa ɗanda musuluncinsu ba i hana su abin da musulunci ya hana ba, za su

tãshi da shũ ɗãyen idanu (za su tãshi da cutar ido (glaucoma)). Za su tãshi suna dã nã

sani (nad ãma), sannan sai su ɗan koma gefe guda kamar masu shawara. Sai suce wa

junansu, a cikin ra ɗa, “ba mu zauna ba a cik in dũniya face kwana goma”. Sannan

kuma muka yi awa ɗãya a cikin kabari.” Sai wa sunsu suce “ai ba mu zauna a dũniya

ba face yini guda.”

32. mai hana ha ɗuwar ruwan dã ɗi da na zartsi.

42

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 40 A rãnar da ake hũrãwa a cikin ƙãho kuma Munã tãra mãsu laifi, a rãnar nan, sunã

mãsu shũɗãyen idãnu. Suna ɓõy e magana a tsakãninsu, (Sunã ce wa jũna) "Ba ku

zauna ba (a cikin dũniya) fãce kwãna gõma."

Mu ne mafi sani ga abin da suke faɗa a sa´ad da mafĩficinsu ga hanya ke cewa, "Ba

ku zauna ba fãce yini guda." (20:102 -104)

Allah Mai iko ! Har masu laifi sun mance shekarun d a suka yi suna zalunci! Idan m ãye

ya mance, ai uwar „ya ba za ta manta ba, Idan wa ɗanda suka yi z ãlunci sun mance,

waɗanda aka z ãlunta ba za su manta ba, kuma za su faɗa33 domin a fitar musu da

hakkinsu.

Garga ɗi:

Kuma a rãnar da Sa´a ke tsayuwa, mãsu laifi na rantsuwã (suna cewa) b a su zauna a

cikin kabari ba fãce sã´a guda. Kamar haka suka kasance anã karkatar da su. Kuma

waɗanda aka bai wa ilmi da ĩmãni suka ce: "Lalle, haƙĩƙa kun zauna a cikin Littãfin

Allah, har zuwa rãnar tãyarwa, to, kuma wannan ita ce rãnar tãyarwar, kuma amma kũ,

kun kasance ba ku sani ba." To, a rãnar nan uzurin waɗanda suka yi zãlunci bã ya

amfaninsu, kuma bã a neman yardarsu. (30:55 -57)

Wassu masu laifin kuma , idan sun fito daga kabari sai k õwa yai nufi nasa wuri, ba za

su tambayi j ũnansu ba, sabõda sun san abinda suka aikata na hõlewa a rãyuwa rsu ta

dũniya . A wannan ranar b ãbu dangantaka a tsakaninsu. Wannan nau‟in, t ãshinsu ya

kasance k ĩshiyar t ãshin waɗanda nayi b ayãni a sama. A ta ƙaice tashin su ya kas ance

kamar yadda Allah (S WA) Ya ce:

Sa´an nan idan an yi bũsa a cikin ƙaho, to, bãbu dangantakõki a tsakãninsu a rãnar

nan kuma bã zã su tambayi jũnansu ba. (23:101)

Garga ɗi:

Yã kũ waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa, kuma ku kasance tãre da mãsu

gaskiya. (9:119)

Dũkiya da ɗiya, sũ ne ƙawar rãyuwar dũniya, kuma ayyuka mãsu wanzuwa na ƙwarai

sun fi zama alheri a wurin Ubangijinka ga lãda kuma sun fi alheri ga bũri. (18:46)

33. ( وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْٛ ) بِأَيّْ ذَنْبٍ قُتِلَتْ

43

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 41

Dukkan mutanen da suka tãke sani, sun yi kama da mutanen da suka cewa Annabi

(SAW) “Mun san gaskiya ka ke faɗa, yarda ne ba za muyi ba.” Yana daga cikinsu

masu cewa: kabarin mu ɗaya?, idan wani yayi musu nasiha.

Irin waɗannan mutanen za su t ãshi daga kabarinsu, alh ãli dã suna barci a cikin kabarin

bã tãre da ana yi musu az ãba ba, sai su r ũga da gudu suna hak ĩ. Kafin su kai ga wajen

tãruwarsu sai suce “Y ã bõnenmu! W ãne ne ya t ãyar damu daga barcinmu? Sannan sai

su tamb ãya! “ko wannan shi ne wa‟adin da ma nzanni ke ba mu labari? Suce: Lalle

Mazanni sunyi gaskiya:

( وَنُفِخَ فِي الصُّورِ فَإِذَا ىُمْ مِنَ اْلَْجْدَاثِ إِلَى رَبّْهِمْ يػَنْسِلُوفَٔ٘ ) قَالُوا يَاوَيػْلَنَا مَنْ

بػَعَثػَنَا مِنْ مَرْقَدِنَا ىَذَا مَا وَعَدَ الرَّحْمَنُ وَصَدَؽَ الْمُرْسَلُوفَ (ٕ٘ )

Kuma aka yi bũsa a cikin ƙaho, to, sai gã su, daga kaburbura zuwa ga Ubangijinsu,

sunã ta gudu. Suka ce: "Yã bonenmu! Wãne ne ya tãyar da mu daga barcinmu?"

(ashe) "Wannan shi ne abin da Mai rahama ya yi wa´adi da shi, kuma Manzanni sun

yi gaskiya." (36:51 -52)

Garga ɗi:

Kuma sunã cewa, "A yaushe wannan wa´adi yake (aukuwa) idan kun kasance mãsu

gaskiya?" Bã su jiran (kõme) fãce wata tsãwa guda, zã ta kãma su, alhãli kuwa sunã

yin husũma. Bã zã su iya yin wasiyya ba, kuma bã zã su iya kõmãwa zuwa ga iyãlansu

ba. (36:48 -50)

Ba ta kasance ba fãce wata tsãwa ce guda, sai gã su duka, sunã abin halartarwa a gare

Mu. To, a yau, bã zã a zãlunci wani rai da kõme ba. Kuma bã zã a sãkã muku ba fãce

da abin da kuka kasance kunã aikatãwa. (36:53 -54)

Duk wanda ya bijire daga ambaton Allah (wato al ƙur‟ani), da mai yawan aikata bidi‟a,

da fasiƙai, za su t ãshi kamar yadda Allah (SWA) Ya ce: "Kuma wanda ya bijire daga

ambatõNa (Alƙur´ãni) to, lalle ne rãyuwa mai ƙunci ta tabbata a gare shi, kuma

Munã tãyar da shi a Rãnar Ƙiyãma yanã makã ho." (Za) Ya ce: "Ya Ubangiji! Don me

Ka tãyar da ni makãho alhãli kuwa nã kasance mai gani?" (Allah) Ya ce: "Kamar

wancan ne ãyõyinMu suka je maka sai ka mance su, kuma kamar haka a yau ake

mance ka."

44

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 42 Allah (SWA) Ya ce: Kuma kamar haka Muke sãka wa wanda ya yawaita (lalata

rãyuwa rsa), kuma bai yi ĩmãni da ãyõyin Ubangijinsa ba. Kuma lalle ne azãbar

Lãhira ce mafi tsanani, kuma mafi w anzuwa (20:124 -127)

Garga ɗi:

Kuma kada ku zãgi wa ɗanda suke kira, baicin Allah, har su zãgi Allah bisa zãlunci, ba

da ilmi b a. Kamar wannan (misalin) ne Muka ƙ ãwata ga kõwace al´umma34 aikinsu,

sa´an nan zuwa ga Ubangijinsu makõmarsu take, sa´an nan Ya ba su lãbari da abin da

suka kasance sunã aikatãwa. (6:108)

Masu cin riba (ko b ãyarwa) ta kowac e hanya - har ma ta hanyar kar ɓan bãshin kuɗi a

banki, ko ajiya a deposit account (marar shara ɗin juya ku ɗi da raba riba) - zã su tãshi

daga kabarinsu kamar masu farf ãɗiya ( epilepsy ). Suna t ãshi suna f ãɗuwa, sannan ga

tangaɗi da tashin hankali! To sabõda me yasa suka t ãshi a irin wannan hali?

Wancan, dõmin lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba yake."

Garga ɗi:

Waɗanda suke cin riba b ã su tãshi, fãce kamar yadda wanda Shaiɗan yake ɗimautarwa

daga shafa yake t ãshi. Wancan, dõmin lalle ne sun ce: "Ciniki kamar riba yake."

Kuma Allah Y ã halatta ciniki kuma Y ã haramta riba. To, wanda wa´azi daga

Ubangijinsa, ya je masa, sa´an nan ya hanu, to yana da abin da ya shige, kuma

al´amarinsa (ana wakkala shi) zuwa ga Allah. Kuma wanda ya kõma, to, waɗannan sũ

ne abõkan Wuta, sũ a cikinta madawwama ne.

Allah Yana shãfe albarkar riba, kuma Yana ƙãra (albarkar) sadakõki. Kuma Allah bã

Ya son du kkan mai yawan kãfirci, mai zunubi. (2:275 -276)

Yã ku waɗanda suka yi ĩmãni! Ku bi Allah da taƙawa kuma ku bar abin da ya rage

daga riba, idan kun kasance mãsu ĩmãni. To, idan ba ku aikata ba, to ku sani fa, da

akwai yãƙi daga Allah da ManzonSa. Kuma idan kun tũba to kuna da asalin

dũkiyõyinku, bã ku zãlunta, kuma bã a zãluntar ku. (2:278 -279)

Yã ku wa ɗanda suka yi ĩmãni! Kada ku ci riba n inki-ninki, riɓanye. kuma ku bi Allah

da taƙawa, tsammãninku zã ku ci nasara. Kuma ku ji tsõron wutã wadda aka yi tattali

dõmin kãfirai. Kuma ku yi ɗã´a ga Allah da ManzonSa, tsammaninku a yi muku

rahama. (3:130 -132)

34. Al’ummar akidar: Sh ĩ’a, Ɗarika da sauransu.

45

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 43

Dukkan wanda ya kasance f ãjiri, kuma bai daidaita a tsakanin matansa ba, bai daidaita

a tsakanin „ya‟yansa ba, to wannan zai t ãshi daga kabarinsa ya r ũga da gudu zuwa

wajen mai busa. ƙũra za ta rufe shi don tsananin wahalar gudu, sannan fuskarsa za ta

zama baƙa sõsai. Daga zarar wannan mutum ya hangi wani daga cikin uwarsa ko

ubansa ko iyalensa ko wani ɗan-uwansa, sai ya lalla ɓa ya gudu daga wurin don kada

su haɗa idãnu . Ga Kõwane mutum daga cikinsu (iyalai f ãjirai) akwai wani sha’ani d a

ya ishe shi35 a wannan ranar.

Garga ɗi:

To, idan mai tsãwa (b ũsa ta biyu) ta zo. Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan´uwansa.

Da uwarsa da ubansa. Da mãtarsa da ɗiyansa. Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar

nan akwai wani sha´ani da ya ishe shi.

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne. Mã su dãriya ne, mãsu bushãra. Wasu

huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu. Baƙi zai rufe su. Waɗannan sũ ne kãfirai

fãjirai (ga ayyukansu). (80:33 -42)

Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Kada dũkiyõyinku da ɗiyanku su shagaltar da ku daga

ambaton Allah. Kuma wand a ya yi haka, to, waɗannan sũ ne mãsu hasãra. (63:9)

Kuma idan wata mace ta ji tsõron ƙiyo daga mijinta kõ kuwa bijirewa to, bãbu laifi a

kansu su yi sulhu a tsakãninsu, sulhu (mai kyau). Kuma yin sulhu ne mafi alheri.

Kuma an halartar (an ƙãwata) wa rayũ ka yin rõwa. Kuma idan kun kyautata, kuma

kuka yi taƙawa, to, lalle ne, Allah Yã kasance, ga abin da kuke aikatãwa, Masani.

Kuma bã zã ku iya yin ãdalci ba a tsakanin mãtã kõ dã kun yi kwaɗayin yi. Sabõda

haka kada ku karkata dukkan karkata, har ku bar ta (dãya matar) kamar wadda aka

rãtaye36 Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taƙawa, to, lalle ne Allah Yã kasance

Mai gãfara, Mai jin ƙai. (4:128 -129)

Kuma idan kun yi nufin musanya mãta a matsayin wata mãta37, alhãli kuwa kun bai

wa ɗ ãyarsu38 ƙinɗãri39 to kada ku karɓi kõme daga gare shi. Shin zã ku karɓe shi da

ƙarya da zunubi bãyyananne? Kuma yãyã zã ku karɓe shi alhãli kuwa, haƙĩƙa,

sãshenku yã sãdu zuwa ga sãshe, kuma sun riƙi al ƙawari mai kauri daga gare ku?

(4:20 -21)

Saki sau biyu yake, sai a riƙa da a lheri, ko kuwa a sallama bisa kyautatãwa. Kuma b ã

ya halatta a gare ku (maza) ku karɓe wani abu daga abin da kuka bã su, fãce fa idan s ũ

35. Duba aya ta 80:37.

36. kamar rãg aya wacce aka r ãtaye ba a komai da ita sai ajiyar kãya n miya .

37. Idan kunyi nufin sabon aure .

38. wacce za’a musanyan .

39. tãrin d ũkiya.

46

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 44 (ma´auran) na tsõron bã zã su ts ãyar da iyãkõkin Allah ba. Idan (k ũ danginsu) kun ji

tsõron bã zã su ts ãyar da iyãkõkin Allah ba, to, bãbu laifi a kansu a cikin abin da ta yi

fansa da shi. Waɗancan iyãkõkin Allah ne sabõda haka kada ku ƙetare su. Kuma

wanda ya ƙetare iyãkõkin Allah, to waɗannan su ne azzãlumai. (2:229)

Mace mai j ũna biyu wacce ta mutu tana s ãɓon Allah, z ã ta haifu a wannan ranar

sabõda tsananin wahala, daga z ãrar ta tashi daga kabarinta.

Mai sh ãyarwa, wacce ta mutu tana sãɓon Allah, za ta shagala da tambayar jãririnta

bãyan ta t ãshi daga kab arinta.

Sauran masu laifi kamar laifin shan giya da caca da sauransu, za su t ãshi daga

kaburburansu suna tanga ɗi, kamar sun sha giya, sabõda tsananin wahala.

Garga ɗi:

Yã ku mutãne! Ku bi Ubangijinku da taƙawa. Lalle ne girgizar ƙasa ta tsayuwar Sa´a

wata aba ce mai girma.

A rãnar da kuke ganin ta, dukkan mai shãyar da mãma tanã shagala daga abin da ta

shãyar, kuma dukan mai ciki tanã haihuwar cikinta, kuma kanã ganin mutãne sunã

mãsu mãye alhãli kuwa su bã mãsu mãye ba, amma azãbar Allah ce mai tsanani.

(22:1-2)

Ya ku waɗanda suka yi ĩmãni! Abin sani kawai, giya da cãca da refu da kiban ƙuri´a,

ƙazanta ne daga aikin shaiɗan, sai ku nĩsance shi, wa la´alla ku ci nasara. Abin sani

kawaĩ Shaiɗan yanã nufin ya aukar da adãwa da ƙeta a tsakãninku, a cikin giya da

cãca, kuma ya kange ku daga ambaton Allah, kuma daga sallah. To, shin, ku mãsu

hanuwa ne? Ku yi ɗã´a ga Allah, kuma ku yi ɗã´a ga Manzo, kuma ku kiyãye. To, idan

kun jũya, to, ku sani abin da kawai yake kan ManzonMu, iyarwa bayyananniya. (5:90 -

92)

Ba dukkan yara ƙanana da suka mutu ba ne „yan aljanna! An tambayi Manzon Allah

(SAW) akan tsatson mushirikai (kafirai), (shin za su shiga aljanna?” ) sai yace: “Allah

(Masanin gaibu) Shi ne yasan abin da za su aikata (da sun girma).40

وعن ابن مسعود قاؿ: قاؿ رسوؿ اهلل صلى اهلل عليو وسلم: ((الوائدة والموؤدة في النار))

40. Daga Nana Aisha (R.A), Ruw ãyar Ab ũ Dauda.

47

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 45 Samãri da „yan m ãta (masu laifi) idan sun t ãshi daga kabari za su nufi wajen mai busa

da gudu. Kafin su ƙãrasa wajen mai b ũsa, sai launin g ãshin kansu ya canza zuwa far ĩ

sabõda wahala :

To, yãya, idan kun kãfirta, zã ku kãre (azabar) wani yini mai m ãyar da yãra (ts õfaffi)

mãsu hurhura. (73:17)

Garga ɗi:

Shin wanin Addinin Allah suke nema, alhãli kuwa a gare Shi ne waɗanda ke cikin

sama da ƙasa suka sallama wa, a kan sõ da ƙĩ , kuma zuwa gare Shi ake m ãyar da su?

(3:83)

Ku ce: "Mun yi ĩmãni da Allah, da abin da aka sau ƙar zuwa gare mu, da abin da aka

sauƙar zuwa ga Ibrãhĩm da Ismã´ĩla da Is´hãƙa da Ya´aƙũbu da jĩkõki, da abin da aka

bai wa Mũsã da Ĩsã, da abin da aka bai wa an nabãwa daga Ubangijinsu, bã mu

rarrabewa a tsakãnin kõwa daga gare su, kuma mu, a gare Shi, mãsu miƙa wuya ne."

(2:136)

Kuma lbrãhĩm y ã yi wasiyya da ita ga ɗiyansa, kuma Ya´aƙũbu (y ã yi wasiyya, suka

ce:) "Yã ɗiyãna! Lalle ne, Allah Y ã zãɓã muku addini don haka kada ku mutu, lalle,

fãce kuna Musulmai." (2:132)

ãyan an t ãru a wajen mai busa, zã ka ga wassu mutane suna m ãsu jin ts õro, suna

raɗa a jũnansu, suna cewa “wai! Ashe lalle za‟a iya m ãyar da mu akan sawunmu?

Dã (a dũniya ) mun kasance muna cewa i dan mun mutu mun kasance ƙasusuwa

rududdugaggu ba za a t ãyar da mu ba.”

Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne. Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu. Sunã

cewa "Ashe lalle zã a iya m ãyar da mu a kan sãwunmu? "Ashe, idan muka zama

ƙasusuwa rududdugaggu?"

(Dã, a d ũniya ) Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!" (79:8 -12)

Garga ɗi:

Yã nadãma a kan bãyĩNa! Wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã

mãsu yi masa izgili. Ba su gani ba, da yawa Muka halakar da (mutãnen) ƙarnõni a

gabãninsu kuma cewa su bã zã su kõmo ba? Kuma lalle bãbu kõwa fãce waɗanda ake

halartarwa ne a wurinMu. Kuma ãyã ce a gare su: Ƙasã matacciya, Mu rãyar da ita,

Mu fitar da ƙwãya daga gare ta, sai gã shi daga gare ta suke ci. Kuma Muka sanya, a

cikinta (ƙasã), waɗansu gõnaki na dabĩno da inabõbi, kuma Muka ɓuɓɓugar da ruwa

daga maremari a cikinta. B

48

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 46 Dõmin su ci ´ya´yan itãcensa, alhãli kuwa hannãyensu ba su aikata shi ba. Shin, to, bã

zã su gõde ba? Tsarki ya tabbata ga Wanda Ya halitta nau´uka, namiji da mace,

dukkansu, daga abin da ƙasã ke tsirarwa, kuma daga kansu, kuma daga abinda ba su

sani ba. (36:30 -36)

aga z ãrar mut ãne da sauran halittu sun hallara, sama za ta ts ãge. Malã‟iku za su

kasance akan s ãsanin sama, sama da wa ɗannan malã‟iku akwai wassu malã‟iku

guda takwas wa ɗanda suke ɗauke da al‟arshin Ubangiji (SWA) . Bãbu wani rai da zai

iya ɓũya a ranar nan , kuma ba wurin ɓũya. Ranar nan, kawai, sai g ã halittu suna

tsattsaye suna kallon ikon Allah.

A ran nan, mai aukuwa zã ta auku. Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai

rauni ce. Kuma malã´iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã´iku)

takwas na ɗauke da Al´arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar. A rãnar

nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda

zai iya ɓõyew a. (69:15 -18)

Garga ɗi:

Kuma a rãnar da sama take tsattsãgewa tãre da gizãgizai, kuma a sau ƙar da malã´iku,

sauƙarwa. Mulki a rãnar nan, na gaskiya, yanã ga Mai rahama. kuma y ã zama yin i, a

kan kãfirai, mai tsanani. (25:25 -26)

utãne da aljannu tsattsaye suna kallo, sai Allah (SWA) Ya ce: “Ya jama’ar

aljannu da mutane! Idan kuna iya zarcewa daga sasanin sammai da kasa, to

ku zarce…41

Allah ma ɗaukakin Sarki Zai ce: “ Lalle ne, ha ƙiƙa , kun zo mana ɗai-ɗai, kamar

yadda Muka halitt ãku a farkon lõkaci , kuma k un bar abin da muka mallaka muku

(na d ũkiya) a b ãyan bãyayyakinku, kuma ba Mu gani a tare da ku ba, macetanku

wadanda kuka riya cewa lalle ne su, a cikinku masu tarayya ( -r taimakon juna) ne.

lalle ne, ha ƙiƙa, kõme ya yayyanke a tsak ãninku, kuma abinda kuk a kasance kuna

riyãwa y ã ɓace daga gareku. (6:94)

utane da aljannu - salihai da mushirikai - duk sunyi shiru suna ji. Daga nan sai a

umarci mutane su rarrabe.

Kuma a rãnar da Sa´a ke tsayuwa, a rãnar nan mutãne ke rarraba.

41. Ibn Kathir ya tafi akan wannan ayar tana magana akan ranar kiyama ne! ba akan mutuwa a nan duniya ba D

M

M

49

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 47 To, amma waɗanda suka yi ĩmãni, k uma suka aikata ayyukan ƙwarai, to sũ anã

faranta musu rãyuka, a cikin wani lambu. Kuma waɗanda suka kãfirta, kuma suka

ƙaryata, game da ãyõyinMu da kuma haɗuwa da Rãnar Lãhira, to, waɗancan anã

halartar da su a cikin azãba. (30:14 -16)

annan kafin his ãbi kenan tukuna. Kamar dai ɓarãwo ne da mai k ãya a kõtu.

Kafin shari‟a ta k ãya, alkali zai sa a tsare ɓarãwo a gidan y ãri sannan a bar mai

kãya ya kwana a duk yadda yaga zai huta. To lõkacin da masu ĩmãni suke cikin wani

lambu wane cikin azãba ake kai ɓarãyi, maƙaryata, azzãlumai?

Garga ɗi:

Lalle ne, mãsu taƙawa suna a cikin inuwõwi da maremari. Da wasu ´ya´yan itãce irin

waɗanda suke marmari. (A ce musu) "Ku ci ku sha cikin ni´ima sabõda abin da kuka

kasance kuna aikatãwa." (77:41 -43)

Kuma waɗannan da suka yi ɗã´a ga Allah da Mazonsa, to waɗannan sunã tãre da

waɗanda Allah Ya yi ni´ima a kansu, daga annabãwa da mãsu yawan gaskatãwa, da

masu shahãda da sãlihai. Kuma waɗannan sun kyautatu ga zama abõkan tafiya.

Waccan falalar daga Allah take, kuma Allah Yã isa zama Masani. (4:69 -70)

Sabõda haka: Ka ts ãyar da sallah a karkatar rãnã zuwa ga duhun dare da lõkacin fitar

alfijir, lalle ne karãtun fitar alfijir ya kasance wanda ake halarta. Kuma da dare, sai ka

yi hĩra da shi (Alƙur´ãni) akan ƙãri gare ka. Akwai tsa mmãnin Ubangijinka Ya tãyar

da kai a wani matsayi gõdadde. (17:78 -79)

zãbar da k ãfirai za su shiga a r ãnar nan , ita ce az ãbar wata inuwar bishiya mai

rassa uku. Ita wannan inuwar ba ta da wani sanyi ko ka ɗan. Idan aka kai k ãfirai

inuwar, bishiyar zata r iƙa yin tartatsi (spark) kamar irin na wutar lantarki (electricity).

A duk lõkacin da tayi tart satsi, za ta jefo musu da wani abu kamar ɗigo (drop s) na

narkekkiyar dalma, girmansu kuma kamar ba ƙãƙen rãƙumma manya. Idan tart satsi ya

fãɗo ya danne kãfiri , kãfiri yana ƙonewa, da ƙyar zai tũre wannan tartatsin, kafin kuma

wani ya f ãɗo masa. Allah Y a kiyaye mu.

Hakanan k ãfirai za suyi ta f ãma da wannan az ãbar, a madadin wajen hũtawarsu, kafin

aje ga ranar hisãbi, sannan su k õma cikin babbar az ãba. A wannan r ãnar za a cewa

kafirai:

Ku tafi zuwa ga abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi! Ku tafi zuwa ga

wata inuwa mai rassa uku. Ita ba inuwar ba, kuma ba ta wadãtarwa daga harshen

wuta. Lalle ne, ita, tanã jifã da tartsatsi kamar sõraye. Kamar dai su raƙumm a ne

baƙãƙe. Bone ya tabbata, a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa! (77:29 -34) W

A

50

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 48 Garga ɗi:

Shin suna jira (ne), fãce dai Allah Ya je musu a cikin wasu inuwõyi na girgije, da

malã´iku, kuma an hukunta al´amarin? Kuma zuwa ga Allah al´amurra ake m ãyar da

su. (2:210)

wannan r ãnar, ab õki ba zai tambayi yadda wani ab õkinsa yake ba.42 Wahalar

kõwa ta ishe shi.

Kãfirai z ã su zauna a wannan hãli na az ãbar bishiya, s ũ kuma waɗanda suka yi imãni

za su zauna a cikin lambu (dausayin raudha ko inuwar al‟arshi) har ya zuwa lõkacin da

za‟a zo da manzanni d õmin su b ãda shaida. To, yãyã, idan Mun zo da shaidu daga

dukkan al´umma, kuma Muka zo da kai (ya Muhammadu) a kan wa ɗannan

(al’ummar), kana mai shaida! (4:41)

Kuma, idan manzanni aka ƙayyade lõkacin tãra su. Domin babbar rãna r da aka yi

wa ajali. Domin rãnar rarrabewa. Kuma, me ya sanar da kai rãnar rarrabewa? B õne

yã tabbata a rãnar nan, ga mãsu ƙaryatãwa! (77:11 -13)

Duk da az ãbar da k ãfirai suke ɗanɗanãwa a ƙarƙashin bishiya ma‟ab õciyar reshe uku,

suna ts õron ace al ƙiyãma z a ta ts ãya- watõ suna tsõron ranar da za‟a yi hisabi „yan

wuta su tafi wuta - sabõda azãbar alƙiyãma tafi az ãbar bishiya mai ra ssa uku.

To, idan gani ya ɗimauta (ya yi ƙyalli). Kuma, watã ya yi husũfi (haskensa ya dushe).

Aka tãra rãnã da watã. Mutum, a rãn nan, zai ce "Ina wurin gudu?" (75:7 -10)

Garga ɗi:

A´aha! bãbu mafaka. Zuwa ga Ubangijinka wurin tabbata, a rãnar nan, yake. Ana gayã

wa mutum, a rãnar nan, abin da ya gab ãtar da wanda ya jinkirtar. Ba haka ba! Mutum,

ga abin da ya shafi kansa, masani ne. Kuma ko da yã jefa uzur õrinsa (bã zã a saurãre

shi ba). (75:11 -15)

Ranar b ũsar ƙaho yini ne mai matu ƙar wahala. Akan k ãfirai ba mai sau ƙi ba ne!43

aga zarar an t ãra manzanni, sai a garga ɗo mut ãne dõmin su zo wajen da za‟a

damƙãwa k õwa litt ãfinsa - wajen da za‟ a yi his ãbin ayyuka da bada shaida .

Innãlillãhi wa innã ilaihi rãji‟u n:

42. Duba aya ta 70:10

43. Ayõyi na 74:9 -10 A

D

51

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 49

Ku ji tsõron wani yini wanda ake m ãyar da ku a cikinsa zuwa ga

Allah, sa´an nan kuma a cikawa kõwane rai abin da ya sanã´anta,

kuma sũ bã a zãluntar su. (2:281)

Mu ha ɗu a

52

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 50

1. FITOWAR DAJJAL

2. SAKKOWAR ANNABI ISA DAN MARYAM (A.S)

3. FITOWAR YAJUJU DA MAJUJU.

4. MANYAN KISFEWAR RANA SAU UKU.

5. HAYAKI DA ZAI LULLUBE SAMA

6. FITOWAR DABBA

7. FITOWAR RANA TA YADDA TAKE FADUWA.

8. WUTA MAI KORAR MUTANE ZUWA MATATTARA .

.

1. Aiko da Annabi Muhammadu (S.A.W) Manzo.

2. Wafatin Annabi Muhammadu (SAW)

3. Tsagewar wata (Ya tsage lokacin Annabi (SAW)

4. Shude war (karewa) Sahabbai masu daraja

5. Budewa (nasara akan) Baitul Mukaddas

6. Mutuwar kare dangi (ya faru a 18 A.H a garin Sham)

7. Yawan bayyanar fitina da nau ‟ikansu.

8. Bayyanar tashoshin TV na satelliate.

9. Labarinsa (SAW) game da aukuwar sabanin Sifaini

10. Bayyanar Khawarijawa.

11. Fitowar masu da‟awar annabta, makaryata

12. Amintuwa da security

13. Bayyanar wuta daga Hijaz

14. Yaki da Turkawa (ya faru a lokacin kilafatu banu Umayya)

15. Bayyanar Azzalumai masu dukan mutane da izga (bulalar bindin saniya ko

makamancinta).

16. Kisan tamore (a kashe mutum haka kawai , mai kisan bai san dalili ba )

17. Tozarta amana da dageta daga zuciya

18. Bibiyar (koyi) da yahudawa da nasara.

19. Baiwa ta haifi uwargijiyarta.

20. Bayyanar mata masu nuna tsaraici da shiga matsattsun kaya.

21. Kauyawa su fara gina gidaje masu Tsawo (a birane)

22. Gaisuwar sallama sai wane da wane za‟a yi musu.

23. R arrabuwar kasuwanci.

24. Tarayyar mace da namiji cikin kasuwanci.

25. Kangewar kasuwanci

26. Shaidar Zur

27. Boyewar shaidar gaskiya.

28. Bayyanar Jahilci.

29. Yawaitar rashin ga skiya da annamimanci.

30. Yankewar sada zumunci

31. Mugayen makonta (neighbours)

53

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 51 32. Bayyanar alfasha.

33. Shakkar gaskiyar amini da amincewa da maha‟inci.

34. Halakar (karewar) Malamai, dattijai, masu hankali da bayyanar yan -daba (sara -suka,

kalare , area boys ) da madadinsu.

35. Rashin tan tance zuwa n dukiya (yaki halal yaki haram)

36. Raba Ganimar Fai‟u bisa zalunci (bisa sabawa shari‟a).

37. Cinye ajiyar (amana) da mutum ya bayar da hana shi ita.

38. (Ibadar) Zakka ta daina faranta zuciyar mutane, saboda fitarta.

39. Neman ilmi ba don neman yardar A llah ba.

40. Fifita mata akan mahaifiya wajen mata da‟a ko biyayya.

41. Kusanto da abokai, da nisantar da iyaye (bishiyar giginya…)

42. Daga sauti a cikin masallatai.

43. Shugabanci (ko wakilcin) Fasiki ga kabilarsu.

44. Makaskanci ya zama shugaban tafiya (kamar ya zama Amirul Hajj).

45. Girmama mutum saboda tsoron (ko kaucewa) sharrinsa.

46. Halasta kida.

47. Halasta kayan Siliki ga mazaje

48. Halasta giya (abun da za‟a sha a fita a hankali)

49. Halasta ma‟azif.

50. Gurin (burin) mutuwa

51. Yawan ridda (f ita a musulunci)

52. Fariya da masallatai masu adon zinari da mutum ya gina.

53. Kawata gidaje da yi musu ado da zinariya (Gold)

54. Yawan tsawa (mai walkiya lokacin damina)

55. Yawan rubuce -rubuce da watsa shi (share)

56. Neman dukiya ta hanyar kwaram d a fariyar iya kalami - magana

57. Watsuwar littattafai, ba Al -kur‟ani ba.

58. Zamanin da za‟a samu yawaitar mahaddatan Alkur‟ani, amma a samu karancin malamai

masu sauran ilmi (al -fukaha)

59. Daukan karatun ilmi a waje n yara (kamar masu zafin -kan akida da dogaro da ra‟ayin

malumansu)

60. Mutuwar faj‟a (lokaci guda)

61. Imaratus Sufaha - Shuwagabanni (ko sarakuna) marasa shiryarwa da bin Sunnah.

62. Kusantar zamani (shekaru suna wucewa da sauri)

63. Mai bada labari ya zan bai dace ba, kuma wawa da fifitashi ak an mafi alherinsa.

64. A wayi gari Luka bn Luka. (kamar nau‟in kwaram) sune masu fantamawa a duniya.

65. Masallatai su zama hanyoyi (zirga -zirga a cikinsu) fiye da sallah.

66. Kasuwanni su zama kusa da kusa.

67. Neman rusa al‟ummar musulmai

68. Turarreniya wajen yin limanci.

69. Mafarkin mumini zai na zama gaskiya.

70. Yawaitar karya.

71. Yawan boye kamanni a tsakanin mutane.

72. Yawan girgizar kasa.

54

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 52 73. Yawaitar mata a duniya.

74. Maza za suyi karanci (su zama kadan) in an kwatanta da yawan mata.

75. Bayyanar alfasha da bayyana ta ba tare da jin kunya b a.

76. Karban lada (kudi) don a karanta alkur‟ani.

77. Yawaitar kiba (kitse) a jikin mutane.

78. Bayyanar mutane masu yin bakace da rashin cikawa.

79. Zalunci irin wanda ake cewa “danniyar kashin dankali”

80. Barin hukunci da abin da Allah (SWA) Ya saukar.

81. Yawaitar Rumawa da karancin Larabawa.

82. Yawaitar dukiya a tsakanin mutane har a rasa mai karban Zakka.

83. Kasa zata fitar da taskokinta (dukiya da aka boye a cikinta)

84. Yawaitar jifa daga sama kamar faruwarsa ga mutanen Annabi Shu‟aibu (A.S)

85. Ruwan sama da ba zai sa kasa ta tsirar d a komai ba.

86. Fitina babba da zata samu Larabawa, ayi ta kashe su.

87. Bishiya za tayi magana ta nuna bayahude a musulmi don ya kashe shi

88. Rigima akan dukiyar da za‟a samu a tafkin al -furat.

89. Daukewar karatun Alkur‟ani daga kirjin mutane.

90. Barin zuwa aikin Hajji.

91. Karewar kabilar Quraishawa.

92. Komawar wassu kabilun Larabawa bautar gumaka.

93. Rusa dakin ka‟aba daga wani mutumin Habasha.

94. Yawaitar aikata bidi‟a

95. Sabbin ababen hawa (na motoci…)

96. Iska mai tafiya da rayukan muminai

97. Gushewar duwatsu daga wajajensu.

98. Rashin raba gad o, rashin farin ciki da ganima.

99. Fitar jinjirin wata da girma kamar kamun kwana biyu.

100. Bayyanar Mahdi.

Wadannan wassu daga cikin alamomin tashin duniya (kanana) kenan. Da yawa daga

cikinsu sun riga sun gabata. Kuma tabbas, ba makawa, sauran da basu faru ba, suna

nan tafe. Labari ne daga bakin wanda baya fadan magana don kansa. (sallal lahu alaihi

wa sallam).

Domin karin haske, sai a nemi littafin da ya jero su, sannan yayi bayaninsu daya bayan

daya, mai suna:

نهاية العالم- أشراط الساعة الصغرى والكبرى (مع صور وخرائط وتوضيحات)

د. محمد بن عبد الرحماف العاريفي

55

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 53 su ne wadanda suke yin imani game da gaibi, kuma suna

tsayar da sallah, kuma suna ciyarwa daga abinda Allah Ya arzuta su. Sune

wadanda suke yin imanai da abinda aka saukarwa Annabi Muhammadu (SAW) -

wato alkur‟ani, kuma suke imani da litta fan da aka saukarwa Annabi Isa d an

Mary amu (AS) da littafan da aka sauk ar wa sauran annabawa .44 Har ila yau,

sune wadanda suke ci yarwa a cikin sauki (lokacin da suke da shi) da cikin

tsanani (lokacin fatara) kuma sune masu hadiyewar fushi, k uma masu yafewa

mutane laifi .45

Sune wadanda suke idan wata masifa ta same su (kamar

asarar dukiya ko rai) sai su ce “Inna lil -lahi wa inna ilaihi raji‟un”46. Duk marar

tawakkali da Allah ba mai hakuri bane!

Sune idan an ambaci Allah sai zukatansu su firgita.

Kuma masu hakuri akan abinda ya same su, masu tsayar da sallah, kuma suna

ciyarwa d aga abinda Allah Ya arzutas u.47 Wadannan yanki ne na masu takawa.

Abin sani kawai, muminai sune wadanda suke idan an ambaci

Allah, zukatansu sukan firgita, kuma idan an karanta ayoyinSa a kansu, sai su

kara musu wani imani, kuma ga Ubangijinsu suke dogara.48 Har yanzu, su ne

wadanda sukayi imani kuma sukayi hijira kuma suka yi jihadi saboda Allah,

kuma suka (ku suke) bada masa ukai, kuma suka yi taimako.49 Sune dai, masu

hani da mummunan aiki kuma masu umarni da alheri, kuma suna tsayar da

sallah, kuma suna bayar da zakka, kuma suna da‟a ga Allah da ManzonSa.50

une wadanda suka tabbata zasu hadu da S

Ubangijinsu .51 Wadannan mutane ba sa ketare haddi saboda tsoron sakamako.

sune masu cika alkawarin Allah kuma basa warware

alkawarin (junansu). Kuma s une masu sadar da abin da Allah Ya yi umarni da

shi domin a sadar , kuma suna tsoron Allah, kuma suna tsoron mummunan

bincike (ranar hisabi). Kuma sune wadanda suka yi hakuri domin neman yardar

ubangijinsu, kuma suka tsaida sallah suka ciyar a asirce da bay yane, kuma suna

44. 2:2-4

45. 3:134

46 2:156

47. 22:35

48. 8:2

49. 8:74

50. 9:71

51. 2:46

56

Al-Mautu wa alãmãtis Sã’ a.

@ b a m a g a j + 2 3 4 7 0 6 7 7 6 6 9 9 4 ( S a k o n t e x t k a d a i )

Page 54 tunkude mummunan aiki da mai kyau.52 Sune wadanda ke sauraren magana,

sa‟an nan subi mafi kyawonta. Wadancan sune Allah Ya shiryar da su, kuma

sune masu hankali.53 Wadancan suna da akibar gida mai kyau. Gidajen Aljannar

zama, suna shiga tare da wadanda suka kyautatu daga iyayensu da matansu da

zuriyyarsu.54

Sune masu rikon kafirai masoya, baicin muminai.55 Sune masu

umarni da abin ki, kuma suna hani daga alheri, kuma suna damkewar

hannayensu (suna rowa) sun ma nce Allah, sai (Allah) Ya mantar da su. Lal le ne

munafukai sune fasikai .56 Sune masu cewa in Allah Ya basu arziki zasu ciyar,

amma idan Ya basu sai suyi rowa.57

Sune masu warware alkawarin Allah daga bayan kullashi, kuma su

yanke abinda Allah Ya yi Umarni da shi a sadar, kuma suna ɓarna a cikin

ƙasa.58 Sune masu kazafi a mata.59

Wanda bai yi hukunci da abinda Allah Ya saukar ba, to

wadannan sune azzalumai.60 (Mai sabawa shari ‟a ya cuci mutane, ya cuci kansa)

Lalle ne kafirai sune Azzalumai .61 Sune wa danda suka nemi wanin

musulunci ya zama addini.62

Sune masu bautar gumaka, ko wata

halittar Allah (SWA), sune masu hulda da al‟jannu (ta hanyar yin sihiri). Sune

yaran masu hulda da al jannu (wato masa mus u da‟a) .63 Riya shirka ce karama ,

kamar yadda yazo a cikin hadi si.

52. 13:19 -22

53. 39:18

54. 39:18 -19

55. 4:139

56. 9:67

57. 9:75 -77

58. 2:27

59. 24:4

60. 5:45

61. 2:254- وَالْكَافِرُوفَ ىُمُ الظَّالِمُوفَ

62. 3:85

63. Duba sura ta; 6:121

— Ƙarshen Littafi —

Mutuwa da Alamomin Tashin Duniya

← Koma ga Bayani